< Jeremiah 29 >
1 These are the words in the scroll that Jeremiah the prophet sent out from Jerusalem to the remaining elders among the captives and to the priests, prophets, and all the people that Nebuchadnezzar exiled from Jerusalem to Babylon.
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 This was after Jehoiachin the king, the queen mother, and the high officials, the leaders of Judah and Jerusalem, and the craftsmen had been sent away from Jerusalem.
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 He sent this scroll by the hand of Elasah son of Shapan and Gemariah son of Hilkiah whom Zedekiah, king of Judah, had sent to Nebuchadnezzar king of Babylon.
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 The scroll said, “Yahweh of hosts, God of Israel, says this to all the captives whom I caused to be exiled from Jerusalem to Babylon,
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 'Build houses and live in them. Plant gardens and eat their fruit.
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 Take wives and give birth to sons and daughters. Then take wives for your sons, and give your daughters to husbands. Let them give birth to sons and daughters and increase there so you do not become too few.
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 Seek the peace of the city where I have caused you to be exiled, and intercede with me on its behalf since there will be peace for you if it is at peace.'
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 For Yahweh of hosts, God of Israel, says this, 'Do not let your prophets who are in your midst and your diviners deceive you, and do not listen to the dreams that you yourselves are having.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 For they are prophesying deceitfully to you in my name. I did not send them—this is Yahweh's declaration.'
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 For Yahweh says this, 'When Babylon has ruled you for seventy years, I will help you and carry out my good word for you to bring you back to this place.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 For I myself know the plans that I have for you—this is Yahweh's declaration—plans for peace and not for disaster, to give you a future and a hope.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 Then you will call to me, and go and pray to me, and I will listen to you.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 For you will seek me and find me, since you will seek me with all your heart.
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 Then I will be found by you—this is Yahweh's declaration—and I will bring back your fortunes; I will gather you from all the nations and places where I scattered you—this is Yahweh's declaration—for I will bring you back to the place from where I caused you to be exiled.'
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 Since you said that Yahweh has raised up prophets for us in Babylon,
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 Yahweh says this to the king who sits on the throne of David and to all the people who are staying in that city, your brothers who have not gone out with you into captivity—
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 Yahweh of hosts says this, 'See, I am about to send sword, famine, and disease on them. For I will make them like rotten figs that are too bad to be eaten.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 Then I will pursue them with sword, famine, and plague and make them a horrible sight to all the kingdoms on earth—a horror, an object of curses and hissing, and a shameful thing among all the nations where I scattered her.
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 This is because they did not listen to my word—this is Yahweh's declaration—that I sent out to them through my servants the prophets. I repeatedly sent them, but you would not listen—this is Yahweh's declaration.'
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 So you yourselves listen to the word of Yahweh, all you exiles whom he has sent out from Jerusalem to Babylon,
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 'Yahweh of hosts, God of Israel, says this about Ahab son of Kolaiah and Zedekiah son of Maaseiah, who prophesy falsely to you in my name: See, I am about to put them into the hand of Nebuchadnezzar king of Babylon. He will kill them before your eyes.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 Then a curse will be spoken about these persons by all the captives of Judah in Babylon. The curse will say: May Yahweh make you like Zedekiah and Ahab, whom the king of Babylon roasted in fire.
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 This will happen because of the shameful things they did in Israel when they committed adultery with their neighbor's wives and declared false words in my name, things that I never commanded them to say. For I am the one who knows; I am the witness—this is Yahweh's declaration.'”
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 “About Shemaiah the Nehelamite, say this:
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 'Yahweh of hosts, God of Israel, says this: Because you sent out letters in your own name to all the people in Jerusalem, to Zephaniah son of Maaseiah the priest, and to all the priests, and said,
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 “Yahweh has made you priest instead of Jehoiada the priest, for you to be in charge of Yahweh's house. You are in control of all the people who rave and make themselves into prophets. You should put them in stocks and chains.
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 So now, why have you not rebuked Jeremiah of Anathoth, who makes himself into a prophet against you?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 For he has sent to us in Babylon and said, 'It will be a long time. Build houses and live in them, and plant gardens and eat their fruit.”'”
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 Zephaniah the priest read this letter in the hearing of Jeremiah the prophet.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 Then the word of Yahweh came to Jeremiah, saying,
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 “Send word to all the exiles and say, 'Yahweh says this about Shemaiah the Nehelamite: Because Shemaiah has prophesied to you when I myself did not send him, and he has led you to believe lies,
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 therefore Yahweh says this: Look, I am about to punish Shemaiah the Nehelamite and his descendants. There will not be a man for him to stay among this people. He will not see the good that I will do for my people—this is Yahweh's declaration—for he has proclaimed rebellion against Yahweh.'”
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”