< Isaiah 7 >
1 During the days of Ahaz son of Jotham son of Uzziah, king of Judah, Rezin the king of Aram, and Pekah son of Remaliah, king of Israel, went up to Jerusalem to war against it, but they could not prevail against it.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 It was reported to the house of David that Aram was allied with Ephraim. His heart trembled, and the heart of his people, as the trees of the forest shake in the wind.
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 Then Yahweh said to Isaiah, “Go out with your son Shear-Jashub to meet Ahaz at the end of the conduit of the upper pool, on the road to Launderer's Field.
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 Tell him, 'Be careful, remain calm, do not be afraid or intimidated by these two smoldering firebrands, by the fierce anger of Rezin and Aram, and of Pekah son of Remaliah.
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 Aram, Ephraim, and the son of Remaliah have planned evil against you; they have said,
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 “Let us attack Judah and terrify her, and let us break into her and set up our king there, the son of Tabeel.”
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 The Lord Yahweh says, “It will not take place; it will not happen,
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 because the head of Aram is Damascus, and the head of Damascus is Rezin. Within sixty-five years, Ephraim will be shattered and will no longer be a people.
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 The head of Ephraim is Samaria, and the head of Samaria is Remaliah's son. If you do not remain firm in faith, surely you will not remain secure.”'”
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 The Lord spoke again to Ahaz,
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 “Ask a sign of Yahweh your God; ask for it in the depths or in the height above.” (Sheol )
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol )
12 But Ahaz said, “I will not ask, nor will I test Yahweh.”
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 So Isaiah replied, “Listen, house of David. Is it not enough for you people to test the patience of people? Must you also test the patience of my God?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 Therefore the Lord himself will give you people a sign: See, the young woman will conceive, bear a son, and will call his name Immanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 He will eat curds and honey when he knows to refuse the evil and choose the good.
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 For before the child knows to refuse the evil and choose the good, the land whose two kings you dread will be desolate.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 Yahweh will bring on you, on your people, and on your father's house days unlike any since Ephraim seceded from Judah—he will bring on you the king of Assyria.”
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 At that time Yahweh will whistle for a fly from the distant streams of Egypt, and for a bee from the land of Assyria.
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 They will all come and settle down into all the gorges, into the clefts of the rocks, on all the thornbushes, and onto all the pastures.
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 At that time the Lord will shave with a razor that was hired beyond the Euphrates River—the king of Assyria— the head and the hair of the legs; it will also sweep away the beard.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 On that day, a man will keep alive a young cow and two sheep,
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 and because of the abundance of milk which they shall give, he will eat curds, for everyone left in the land will eat curds and honey.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 At that time, where there were a thousand vines worth a thousand silver shekels, there will be nothing but briers and thorns.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 Men will go there to hunt with bows, because all the land will be briers and thorns.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 They will stay away from all the hills that were cultivated with the hoe, for fear of the briers and thorns; but it will be a place where cattle and sheep graze.
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.