< Isaiah 64 >

1 “Oh, if you had split open the heavens and come down! The mountains would have shaken at your presence,
Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
2 as when fire kindles the brushwood, or the fire makes water boil. Oh, that your name would be known by your adversaries, that the nations would tremble at your presence!
Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
3 Previously, when you did marvelous things that we had not expected, you came down, and the mountains trembled at your presence.
Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
4 Since ancient times no one has heard or perceived, nor eye seen any God besides you, who does things for him who waits for him.
Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
5 You come to help those who rejoice in doing what is right, those who call to mind your ways and obey them. You were angry when we sinned. In your ways we will always be rescued.
Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
6 For we have all become like one who is unclean, and all our righteous deeds are like a menstrual rag. We have all withered like leaves; our iniquities, like the wind, carry us away.
Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
7 There are none who calls on your name, who makes an effort to take hold of you. For you have hidden your face from us and made us waste away in the hand of our iniquities.
Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
8 Yet, Yahweh, you are our father; we are the clay. You are our potter; and we all are the work of your hand.
Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
9 Be not too angry, Yahweh, nor always call to mind against us our sins. Please look at us all, your people.
Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
10 Your holy cities have become a wilderness; Zion has become a wilderness, Jerusalem a desolation.
Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
11 Our holy and beautiful temple, where our fathers praised you, has been destroyed by fire, and all that was so dear is in ruins.
Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
12 How can you still hold back, Yahweh? How can you remain silent and continue to humiliate us?”
Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?

< Isaiah 64 >