< Isaiah 25 >

1 Yahweh, you are my God; I will exalt you, I will praise your name; for you have done wonderful things, things planned long ago, in perfect faithfulness.
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
2 For you have made the city a heap, a fortified city, a ruin, and a fortress of strangers into no city.
Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
3 Therefore a strong people will glorify you; a city of ruthless nations will fear you.
Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
4 For you have been a place of safety for the one who is poor, a shelter for the one who is needy in his distress— a shelter from the storm and a shade from the heat. When the breath of the ruthless was like a storm against a wall,
Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
5 and like heat in a dry land, you subdued the noise of foreigners, as the heat is subdued by the shade of a cloud, so the song of the ruthless ones is answered.
kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
6 On this mountain Yahweh of hosts will make for all peoples a feast of fat things, of choice wines, of tender meats, a feast on the lees.
A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
7 He will destroy on this mountain the covering over all peoples, the web woven over all the nations.
A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
8 He will swallow up death forever, and the Lord Yahweh will wipe away tears from off all faces; the disgrace of his people he will take away from all the earth, for Yahweh has spoken it.
zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
9 It will be said on that day, “Look, this is our God; we have waited for him, and he will save us. This is Yahweh; we have waited for him, we will be glad and rejoice in his salvation.”
A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
10 For on this mountain the hand of Yahweh will rest; and Moab will be trampled down in his place, even as straw is trampled down in a pit filled with manure.
Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
11 They will spread their hands in the midst of it, as a swimmer spreads his hands to swim. But Yahweh will bring down their pride in spite of the skill of their hands.
Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
12 Your high fortress walls he will bring down to the ground, to the dust.
Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.

< Isaiah 25 >