< Isaiah 24 >

1 Look, Yahweh is about to empty the earth, to devastate it, mar its surface, and scatter its inhabitants.
Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
2 It will come about that, as with the people, so with the priest; as with the servant, so with his master; as with the maid, so with her mistress; as with the buyer, so with the seller; as with the creditor, so with the debtor; as with the receiver of interest, so with the giver of interest.
zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
3 The earth will be completely devastated and completely stripped; for Yahweh has spoken this word.
Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
4 The earth dries up and withers, the world shrivels up and fades away, the prominent people of the earth waste away.
Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
5 The earth is polluted by its inhabitants because they have transgressed the laws, violated the statutes, and broken the everlasting covenant.
Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
6 Therefore a curse devours the earth, and its inhabitants are found guilty. The inhabitants of the earth burn up, and few people are left.
Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
7 The new wine dries up, the vine withers, all the merry-hearted groan.
Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
8 The happy sound of the tambourines stops, and the revelry of those who rejoice; the joy of the lyre ceases.
Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
9 They no longer drink wine and sing, and the beer is bitter to those who drink it.
Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
10 The city of chaos has been broken down; every house is closed up and empty.
Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
11 There is a crying in the streets because of the wine; all joy is darkened, the gladness of the land has disappeared.
A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
12 In the city is left a desolation, and the gate is broken into a ruin.
An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
13 For this is how it will be on the whole earth among the nations, as when an olive tree is beaten, as the gleanings when the grape harvest is done.
Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
14 They will lift up their voices and shout the majesty of Yahweh, and will joyfully shout from the sea.
Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
15 Therefore in the east glorify Yahweh, and in the isles of the sea give glory to the name of Yahweh, the God of Israel.
Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
16 From the farthest part of the earth we have heard songs, “Glory to the righteous one!” But I said, “I have wasted away, I have wasted away, woe is me! The treacherous have dealt treacherously; yes, the treacherous have dealt very treacherously.”
Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
17 Terror, the pit, and the snare are upon you, inhabitants of the earth.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
18 He who flees from the sound of terror will fall into the pit, and he who comes up out of the middle of the pit will be caught in the snare. The windows of the heavens will be opened, and the foundations of the earth will shake.
Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
19 The earth will be completely broken, the earth ripped apart; the earth will be violently shaken.
An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
20 The earth will stagger like a drunken man and it will sway back and forth like a hut. Its sin will be heavy on it and it will fall and never rise again.
Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
21 On that day Yahweh will punish the host of the heaven in the heavens, and the kings of the earth on the earth.
A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
22 They will be gathered together, prisoners in a pit, and will be shut up in a prison; and after many days they will be punished.
Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
23 Then the moon will be ashamed, and the sun disgraced, for Yahweh of hosts will reign on Mount Zion and in Jerusalem, and before his elders in glory.
Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.

< Isaiah 24 >