< Hosea 3 >

1 Yahweh said to me, “Go again, love a woman, loved by her husband, but who is an adulteress. Love her just as I, Yahweh, love the people of Israel, although they turn to other gods and love raisin cakes.”
Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
2 So I bought her for myself for fifteen pieces of silver and a homer and a lethek of barley.
Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
3 I said to her, “You must live with me many days. You will not be a prostitute or belong to any other man. In the same way, I will be with you.”
Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
4 For the people of Israel will live for many days without a king, prince, sacrifice, stone pillar, ephod or household idols.
Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
5 Afterward the people of Israel will return and seek Yahweh their God and David their king, and in the last days, they will come trembling before Yahweh and his goodness.
Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.

< Hosea 3 >