< Haggai 2 >

1 In the seventh month on the twenty-first day of the month, the word of Yahweh came by the hand of Haggai the prophet, saying,
a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
2 “Speak to the governor of Judah, Zerubbabel son of Shealtiel, and to the high priest Joshua son of Jehozadak, and to the remnant of the people. Say,
“Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
3 'Who is left among you who saw this house in its former glory? How do you see it now? Is it not like nothing in your eyes?
‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
4 Now, be strong, Zerubbabel!—this is Yahweh's declaration— and be strong, high priest Joshua son of Jehozadak; and be strong, all you people in the land!—this is Yahweh's declaration— and work, for I am with you!—this is the declaration of Yahweh of hosts.
Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 This is the covenant that I established with you when you came out of Egypt, and my Spirit remains with you. Do not fear!
‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
6 For Yahweh of hosts says this: In a little while I will once again shake the heavens and the earth, the sea and the dry land!
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
7 I will shake every nation, and every nation will bring their precious things to me, and I will fill this house with glory, says Yahweh of hosts.
Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
8 The silver and gold are mine!—this is the declaration of Yahweh of hosts.
‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 The glory of this house will be greater in the future than at the beginning, says Yahweh of hosts, and I will give peace in this place!—this is the declaration of Yahweh of hosts.”
‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
10 On the twenty-fourth day of the ninth month, in the second year of Darius, the word of Yahweh came by Haggai the prophet, saying,
A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
11 “Yahweh of hosts says this: Ask the priests concerning the law, and say,
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
12 'If a man carries meat that is set apart to Yahweh in the fold of his garment, and the fold touches bread or stew, wine or oil, or any kind of food, does it become holy?'” The priests answered and said, “No.”
Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
13 Then Haggai said, “If someone who is unclean because of death touches any of these things, do they become unclean?” The priests answered and said, “Yes, they become unclean.”
Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
14 So Haggai answered and said, “So it is with this people and this nation before me!—this is Yahweh's declaration—and so it is with everything done by their hands. What they offer to me is unclean!
Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
15 So now, think in your minds about the past leading up to this very day. Before stone was placed upon stone in the temple of Yahweh,
“‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
16 how was it then? When you came to a heap of twenty measures of grain, there were only ten; and when you came to the wine vat to draw out fifty measures, there were only twenty.
A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
17 I afflicted you and all the work of your hands with blight and mildew, but you still did not turn to me—this is Yahweh's declaration.
Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
18 Consider from this day forward, from the twenty-fourth day of the ninth month, from the day that the foundation of Yahweh's temple was laid. Consider it!
‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
19 Is there still seed in the storehouse? The vine, the fig tree, the pomegranate, and the olive tree have not produced! But from this day will I bless you!”
Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
20 Then the word of Yahweh came a second time to Haggai on the twenty-fourth day of the month and said,
Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
21 “Speak to the governor of Judah, Zerubbabel, and say, 'I will shake the heavens and the earth.
“Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
22 For I will overthrow the throne of kingdoms and destroy the strength of the kingdoms of the nations! I will overthrow the chariots and their riders; the horses and their riders will fall down, each one because of his brother's sword.
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
23 On that day—this is the declaration of Yahweh of hosts—I will take you, Zerubbabel son of Shealtiel, as my servant—this is Yahweh's declaration. I will make you like a signet ring, for I have chosen you! —this is the declaration of Yahweh of hosts!'”
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< Haggai 2 >