< Genesis 50 >
1 Then Joseph was so distressed that he collapsed on the face of his father, and he wept over him, and he kissed him.
Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
2 Joseph commanded his servants the physicians to embalm his father. So the physicians embalmed Israel.
Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
3 They took forty days, for that was the full time for embalming. The Egyptians wept for him seventy days.
Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
4 When the days of weeping were over, Joseph spoke to the house of Pharaoh, saying, “If now I have found favor in your eyes, please speak to Pharaoh, saying,
Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
5 'My father made me swear, saying, “See, I am about to die. Bury me in my tomb that I dug for myself in the land of Canaan. There you will bury me.” Now let me go up and bury my father, and then I will return.'”
‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
6 Pharaoh answered, “Go and bury your father, as he made you swear.”
Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
7 Joseph went up to bury his father. All the officials of Pharaoh went with him—the elders of his household, all the senior officials of the land of Egypt,
Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
8 with all Joseph's household and his brothers, and his father's household. But their children, their flocks, and their herds were left in the land of Goshen.
da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
9 Chariots and horsemen also went with him. It was a very large group of people.
Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
10 When they came to the threshing floor of Atad on the other side of the Jordan, they mourned with very great and grievous sorrow. There Joseph made a seven-day mourning for his father.
Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
11 When the inhabitants of the land, the Canaanites, saw the mourning in the floor of Atad, they said, “This is a very sad occasion for the Egyptians.” That is why the place was called Abel Mizraim, which is beyond the Jordan.
Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
12 So his sons did for Jacob just as he had instructed them.
Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
13 His sons carried him to the land of Canaan and buried him in the cave in the field of Machpelah, near Mamre. Abraham had bought the cave with the field for a burial place. He had bought it from Ephron the Hittite.
Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
14 After he had buried his father, Joseph returned into Egypt, he, along with his brothers, and all who had accompanied him to bury his father.
Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
15 When Joseph's brothers saw that their father was dead, they said, “What if Joseph holds on to anger against us and wants to repay us in full for all the evil we did to him?”
Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
16 So they commanded the presence of Joseph, saying, “Your father gave instructions before he died, saying,
Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
17 'Tell Joseph this, “Please forgive the transgression of your brothers and their sin when they did evil to you.”' Now please forgive the servants of the God of your father.” Joseph wept when they spoke to him.
Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
18 His brothers also went and lay facedown before him. They said, “See, we are your servants.”
’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
19 But Joseph answered them, “Do not be afraid. Am I in the place of God?
Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
20 As for you, you meant to harm me, but God meant it for good, to preserve the lives of many people, as you see today.
Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
21 So now do not be afraid. I will provide for you and your little children.” He comforted them in this way and spoke kindly to their hearts.
Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
22 Joseph lived in Egypt, together with his father's family. He lived one hundred ten years.
Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
23 Joseph saw Ephraim's children to the third generation. He also saw the children of Machir son of Manasseh, who were placed on the knees of Joseph.
Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
24 Joseph said to his brothers, “I am about to die; but God will surely come to you and lead you up out of this land to the land which he swore to give to Abraham, to Isaac, and to Jacob.”
Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
25 Then Joseph made the people of Israel swear an oath. He said, “God will surely come to you. At that time you must carry up my bones from here.”
Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
26 So Joseph died, 110 years old. They embalmed him and he was placed in a coffin in Egypt.
Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.