< Genesis 34 >
1 Now Dinah, Leah's daughter whom she bore to Jacob, went out to meet the young women of the land.
To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
2 Shechem son of Hamor the Hivite, the prince of the land, saw her and he grabbed her, assaulted her, and slept with her.
Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
3 He was drawn to Dinah, the daughter of Jacob. He loved the young woman and spoke tenderly to her.
Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
4 Shechem spoke to his father Hamor, saying, “Get this young woman for me as a wife.”
Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
5 Now Jacob heard that he had defiled Dinah his daughter. His sons were with his livestock in the field, so Jacob held his peace until they came.
Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
6 Hamor the father of Shechem went out to Jacob to speak with him.
Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
7 The sons of Jacob came in from the field when they heard of the matter. The men were offended. They were very angry because he had disgraced Israel by forcing himself on Jacob's daughter, for such a thing should not have been done.
Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
8 Hamor spoke with them, saying, “My son Shechem loves your daughter. Please give her to him as a wife.
Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
9 Intermarry with us, give your daughters to us, and take our daughters for yourselves.
Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
10 You will live with us, and the land will be open to you to live and trade in, and to acquire property.”
Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
11 Shechem said to her father and to her brothers, “Let me find favor in your eyes, and whatever you tell me I will give.
Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
12 Ask me for as great a bride price and gift as you will, and I will give whatever you say to me, but give me the young woman as a wife.”
Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
13 The sons of Jacob answered Shechem and Hamor his father with deceit, because Shechem had defiled Dinah their sister.
Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
14 They said to them, “We cannot do this thing, to give our sister to anyone who is uncircumcised; for that would be a disgrace to us.
Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
15 Only on this condition will we agree with you: If you will become circumcised as we are, if every male among you is circumcised.
Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
16 Then will we give our daughters to you, and we will take your daughters to ourselves, and we will live with you and become one people.
Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
17 But if you do not listen to us and become circumcised, then we will take our sister and we will leave.”
Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
18 Their words pleased Hamor and his son Shechem.
Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
19 The young man did not delay to do what they said, because he delighted in Jacob's daughter, and because he was the most honored person in all his father's household.
Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
20 Hamor and Shechem his son went to the gate of their city and spoke with the men of their city, saying,
Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
21 “These men are at peace with us, so let them live in the land and trade in it for, really, the land is large enough for them. Let us take their daughters as wives, and let us give them our daughters.
Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
22 Only on this condition will the men agree to live with us and become one people: If every male among us is circumcised, as they are circumcised.
Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
23 Will not their livestock and their property—all their animals be ours? So let us agree with them, and they will live among us.”
Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
24 All the men of the city listened to Hamor and Shechem, his son. Every male was circumcised.
Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
25 On the third day, when they were still in pain, two of the sons of Jacob (Simeon and Levi, Dinah's brothers), each took his sword and they attacked the city that was certain of its security, and they killed all the males.
Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
26 They killed Hamor and his son Shechem with the edge of the sword. They took Dinah from Shechem's house and went away.
Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
27 The other sons of Jacob came to the dead bodies and looted the city, because the people had defiled their sister.
Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
28 They took their flocks, their herds, their donkeys, and everything in the city and in the surrounding fields with
Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
29 all their wealth. All their children and their wives, they captured. They even took everything that was in the houses.
Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
30 Jacob said to Simeon and Levi, “You have brought trouble on me, to make me stink to the inhabitants of the land, the Canaanites and the Perizzites. I am few in number. If they gather themselves together against me and attack me, then I will be destroyed, I and my household.”
Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
31 But Simeon and Levi said, “Should Shechem have dealt with our sister as with a prostitute?”
Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”