< Ezekiel 38 >
1 The word of Yahweh came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, set your face toward Gog, the land of Magog, the chief prince of Meshech and Tubal; and prophesy against him.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
3 Say, 'The Lord Yahweh says this: Behold! I am against you, Gog, chief prince of Meshech and Tubal.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
4 So I will turn you around and set hooks in your jaw; I will send you out with all your army, horses, and horsemen, all of them dressed in full armor, a great company with large shields and small shields, all of them holding swords!
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
5 Persia, Cush, and Libya are with them, all of them with shields and helmets!
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
6 Gomer and all her troops, and Beth Togarmah, from the far parts of the north, and all its troops! Many peoples are with you!
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
7 Get ready! Yes, prepare yourself and your troops assembled with you, and be their commander.
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
8 You will be called after many days, and after some years you will go to a land that has recovered from the sword and that has been gathered from many peoples, gathered back to the mountains of Israel that had been a continuous ruin. But the land's people will be brought out of the peoples, and they will live in safety, all of them!
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
9 So you will go up as a storm goes; you will be like a cloud covering the land, you and all your troops, all the many soldiers with you.
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
10 The Lord Yahweh says this: It will happen on that day that plans will form in your heart, and you will devise wicked schemes.'
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
11 Then you will say, 'I will go up to the open land; I will go to the quiet people living in safety, all of them living where there are no walls or bars, and where there are no city gates.
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
12 I will capture booty and steal plunder, in order to bring my hand against the ruins that are newly inhabited, and against the people gathered from the nations, people who are gaining livestock and property, and who are living at the center of the earth.'
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
13 Sheba and Dedan, and the traders of Tarshish along with all its young warriors will say to you, 'Have you come to plunder? Have you assembled your armies to take away spoil, to carry off silver and gold, to take their livestock and property and to haul away much plunder?'
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
14 Therefore prophesy, son of man, and say to Gog, 'The Lord Yahweh says this: On that day, when my people Israel are living securely, will you not learn about them?
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
15 You will come from your place far away in the north with a great army, all of them riding on horses, a great company, a large army.
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
16 You will attack my people Israel like a cloud that covers the land. In the latter days I will bring you against my land, so the nations might know me when I show myself through you, Gog, to be holy before their eyes.
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
17 The Lord Yahweh says this: Are you not the one of whom I spoke in former days by the hand of my servants, the prophets of Israel, who prophesied in their own time for years that I would bring you against them?
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
18 So it will come to be in that day when Gog attacks the land of Israel—this is the Lord Yahweh's declaration—my wrath will mount up in my anger.
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
19 In my zeal and in the fire of my anger, I declare that on that day there will be a great earthquake in the land of Israel.
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
20 They will shake before me—the fish of the sea and the birds of the skies, the beasts of the fields, and all the creatures that crawl on the earth, and every person who is on the surface of the land. The mountains will be thrown down and the cliffs will fall, until every wall falls to the earth.
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
21 I will summon a sword against him on all my mountains—this is the Lord Yahweh's declaration—each man's sword will be against his brother.
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
22 Then I will judge him by plague and blood; and overflowing rain and hailstones and burning sulfur I will rain down upon him and his troops and the many nations that are with him.
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
23 For I will show my greatness and my holiness and I will make myself known in the eyes of the many nations, and they will know that I am Yahweh.'”
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’