< Ezekiel 2 >
1 He said to me, “Son of man, stand up on your feet; then I will speak to you.”
Ya ce mini, “Ɗan mutum, tashi ka tsaya a ƙafafunka zan kuma yi maka magana.”
2 Then, as he spoke to me, the Spirit entered into me and set me on my feet, and I heard him speaking to me.
Yayinda yake magana, sai Ruhu ya sauko mini ya kuma tā da ni a ƙafafuna, na kuma ji shi yana mini magana.
3 He said to me, “Son of man, I am sending you to the people of Israel, to rebellious nations that have rebelled against me—both they and their ancestors have sinned against me up to this very day!
Ya ce, “Ɗan mutum, ina aikan ka zuwa ga Isra’ilawa, zuwa ga al’ummar’yan tawayen nan da suka yi mini tayarwa; su da kakanninsu sun yi mini tawaye har yă zuwa yau.
4 Their descendants have stubborn faces and hard hearts. I am sending you to them, and you will say to them, 'This is what the Lord Yahweh says.'
Mutanen da nake aikan ka masu ƙin ji ne da kuma taurinkai. Ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’
5 Either they will listen or they will not listen. They are a rebellious house, but they will at least know that a prophet has been among them.
Kuma ko su ji ko kada su ji, gama su gida ne mai tawaye, za su san cewa akwai annabi a cikinsu.
6 You, son of man, do not be afraid of them or their words. Do not be afraid, although you are with briers and thorns and although you live with scorpions. Do not fear their words or be dismayed by their faces, since they are a rebellious house.
Kai kuwa, ɗan mutum, kada ka ji tsoro, ko da sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa duk sun kewaye ka kana kuma zama a cikin kunamai. Kada ka ji tsoron abin da za ka faɗa ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gida ne mai tawaye.
7 But you will speak my words to them, whether they listen or not, because they are most rebellious.
Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su’yan tawaye ne.
8 But you, son of man, listen to what I am saying to you. Do not be rebellious like that rebellious house. Open your mouth and eat what I am about to give to you!”
Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da zan faɗa maka. Kada ka yi tawaye kamar wannan gidan’yan tawaye; ka buɗe bakinka ka kuma ci abin da na ba ka.”
9 Then I looked, and a hand was extended out to me; in it was a written scroll.
Sai na duba, na kuma ga hannu ya miƙe zuwa wurina. A cikinsa akwai littafi,
10 He spread it out before me; it had been written on both its front and back, and written on it were lamentations, mourning, and woe.
wanda ya nannaɗe a gabana. A kowane gefensa akwai rubutun kalmomin makoki da kuka da kuma kaito.