< Ezekiel 16 >

1 Then the word of Yahweh came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, inform Jerusalem about her abominations,
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 and declare, 'The Lord Yahweh says this to Jerusalem: Your beginning and your birth took place in the land of Canaan; your father was an Amorite, and your mother was a Hittite.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 On the day of your birth, your mother did not cut your navel, nor did she purify you in water or rub you down with salt, or wrap cloth around you.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 No eye had compassion for you to do any of these things for you, to be compassionate toward you. On the day that you were born, with loathing for your life, you were thrown out into the open field.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 But I passed by you, and I saw you writhing in your own blood; so I said to you in your blood, “Live!” I said to you in your blood, “Live!”
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 I made you grow like a plant in a field. You multiplied and became great, and you became the jewel of jewels. Your breasts became firm, and your hair grew thick, though you had been naked and bare.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 I passed by you again, and I saw you. See! the time of love came for you, so I spread my robe over you and covered your nakedness. Then I swore to you and brought you into a covenant—this is the Lord Yahweh's declaration—and you became mine.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 So I washed you with water and rinsed your blood off you, and I anointed you with oil.
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 I dressed you in embroidered clothes and placed leather sandals on your feet. I wrapped you with fine linen and covered you with silk.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Next I adorned you with jewelry, and I put bracelets on your hands, and a chain around your neck.
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 I put a nose ring in your nostrils and earrings in your ears, and a beautiful crown on your head.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 So you were adorned with gold and silver, and you were dressed in fine linen, silk, and embroidered clothes; you ate fine flour, honey, and oil, and you were very beautiful, and you became a queen.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Your fame went out among the nations because of your beauty, for it was perfect in the majesty that I had given to you—this is the Lord Yahweh's declaration.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 But you trusted in your own beauty, and you acted like a prostitute because of your fame; you poured out your acts of prostitution on everyone who passed by, so that your beauty became his.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Then you took your clothes and with them you made high places for yourself decorated in various colors, and there you acted like a prostitute. This should not have happened. Nor should such a thing exist.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 You took the fine jewels of the gold and silver that I gave you, and you made for yourself male figures, and you did with them as a prostitute would do.
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 You took your embroidered garments and covered them, and you set my oils and perfumes before them.
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 My bread I gave you—made with fine flour, oil, and honey—you set before them for a fragrant aroma, for this is what happened—this is the Lord Yahweh's declaration.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Then you took your sons and daughters whom you bore for me, and you sacrificed them to the images to be devoured as food. Are your acts of prostitution a small matter?
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 You slaughtered my children to the idols and made them pass through the fire.
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 In all your abominations and your acts of prostitution you have not thought about the days of your youth, when you were naked and bare as you thrashed about in your blood.
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 Woe! Woe to you!—this is the Lord Yahweh's declaration—therefore, in addition to all this wickedness,
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 you built yourself a vaulted chamber in every public place.
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 You built your high place at the head of every road and made your beauty a disgrace, and you spread your legs to anyone who passed by, and you multiplied your acts of prostitution.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 You have acted like a prostitute with the Egyptians, your lustful neighbors, and you committed many more acts of prostitution, provoking me to anger.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 See! I will strike you with my hand and cut off your food. I will hand your life over to your enemies, the daughters of the Philistines, who were ashamed of your obscene behavior.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 You have acted like a prostitute with the Assyrians because you could not be satisfied. You acted like a prostitute and still were not satisfied.
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 You performed many more acts of prostitution in the land of the merchants of Chaldea, and even this did not satisfy you.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 How sick is your heart—this is the Lord Yahweh's declaration—that you would do all these things, deeds of a shameless prostitute?
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 You have built your high places at the head of every street and made your vaulted chamber in every public place. Yet you were not like a prostitute because you refused to take payment.
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 You adulterous woman, you accept strangers instead of your husband.
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 People give payment to every prostitute, but you give your wages to all your lovers and bribe them to come to you from all around for your acts of prostitution.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 So there is a difference between you and those other women, since no one goes to you to ask you to sleep with them. Instead, you pay them. No one pays you.
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 Therefore, you prostitute, listen to the word of Yahweh.
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 The Lord Yahweh says this: Because you have poured out your lust and uncovered your nakedness through your acts of prostitution with your lovers and with all your detestable idols, and because you gave them your children's blood,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 therefore, behold, I will gather all your lovers that you have met, all those whom you loved and all those whom you hated, and I will gather them against you on every side. I will uncover your nakedness to them so they see all your nakedness.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 For I will punish you for adultery and the shedding of blood, and I will bring on you the bloodshed of my anger and passion.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 I will give you into their hands so they will throw down your vaulted chamber and break down your high places and they will strip you of your clothes and take all of your jewelry. They will leave you naked and bare.
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Then they will bring up a crowd against you and stone you with stones, and they will cut you apart with their swords.
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 They will burn your houses and will perform many acts of punishment on you in the sight of many women, for I will put a stop to your prostitution, and you will no longer pay your lovers.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 Then I will calm my fury against you; my anger will leave you, for I will be satisfied, and will no longer be angry.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 Because you did not call to mind the days of your youth and have made me shake with anger because of all these things, therefore, behold! I myself will bring down on your own head the punishment for what you have done—this is the Lord Yahweh's declaration. Have you not added prostitution to all your other detestable practices?
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Behold! Everyone who speaks proverbs concerning you will say, “As the mother is, so also is her daughter.”
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 You are the daughter of your mother, who detested her husband and her children, and you are the sister of your sisters who detested their husbands and their children. Your mother was a Hittite, and your father was an Amorite.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Your older sister was Samaria and her daughters were the ones living in the north, while your younger sister was the one living south of you, that is, Sodom and her daughters.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 You not only walked in their ways and copied their behavior and practices, but in all your ways you have been worse than they were.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 As I live—this is the Lord Yahweh's declaration—your sister Sodom and her daughters, have not done as much evil as you and your daughters have done.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Behold! This was the sin of your sister Sodom that she was arrogant in her leisure, careless and unconcerned about anything. She did not strengthen the hands of the poor and needy people.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 She was arrogant and committed disgusting actions before me, so I took them away just as you have seen.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Neither did Samaria commit even half of your sins; instead, you have done many more disgusting things than they did, and you have shown that your sisters were better than you because of all the disgusting things that you do!
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Especially you, show your own shame; in this way you have shown that your sisters were better than you, because of the sins you committed in all those disgusting ways. Your sisters now seem better than you. Especially you, show your own shame, for in this way you have shown that your sisters were better than you.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 For I will restore their fortunes—the fortunes of Sodom and her daughters, and the fortunes of Samaria and her daughters; but your fortunes will be among them.
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 On account of these things you will show your shame; you will be humiliated because of everything that you have done, and in this way you will be a comfort to them.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 So your sister Sodom and her daughters will be restored to their former condition, and Samaria and her daughters will be restored to their former estate. Then you and your daughters will be restored to your former condition.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Sodom your sister was not even mentioned by your mouth in the days when you were proud,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 before your wickedness was revealed. But now you are an object of scorn to the daughters of Edom and to all the daughters of the Philistines around her. People all about despise you.
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 You will show your shame and your disgusting actions!—this is Yahweh's declaration!
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 The Lord Yahweh says this: I will deal with you as you deserve, you who have despised your oath by breaking the covenant.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 But I myself will call to mind my covenant with you made in the days of your youth, and I will establish an everlasting covenant with you.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Then you will call to mind your ways and be ashamed when you receive your older sisters and your younger sisters. I will give them to you as daughters, but not because of your covenant.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 I myself will establish my covenant with you, and you will know that I am Yahweh.
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 Because of these things, you will call everything to mind and be ashamed, so you will no longer open your mouth to speak because of your shame, when I have forgiven you for all that you have done—this is the Lord Yahweh's declaration.'”
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ezekiel 16 >