< Exodus 7 >
1 Yahweh said to Moses, “See, I have made you like a god to Pharaoh. Aaron your brother will be your prophet.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 You will say everything that I command you to say. Aaron your brother will speak to Pharaoh so that he will let the people of Israel go from his land.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 But I will harden Pharaoh's heart, and I will display many signs of my power, many wonders, in the land of Egypt.
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 But Pharaoh will not listen to you, so I will put my hand on Egypt and bring out my groups of fighting men, my people, the descendants of Israel, out of the land of Egypt by great acts of punishment.
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 The Egyptians will know that I am Yahweh when I reach out with my hand on Egypt and bring out the Israelites from among them.”
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 Moses and Aaron did so; they did just as Yahweh commanded them.
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 Moses was eighty years old, and Aaron eighty-three years old when they spoke to Pharaoh.
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
8 Yahweh said to Moses and to Aaron,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 “When Pharaoh says to you, 'Do a miracle,' then you will say to Aaron, 'Take your staff and throw it down before Pharaoh, so that it may become a snake.'”
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 Then Moses and Aaron went to Pharaoh, and they did just as Yahweh had commanded. Aaron threw down his staff before Pharaoh and his servants, and it became a snake.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 Then Pharaoh also called for his wise men and sorcerers. They did the same thing by their magic.
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 Each man threw down his staff, and the staffs became snakes. But Aaron's staff swallowed up their snakes.
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 Pharaoh's heart was hardened, and he did not listen, just as Yahweh had foretold.
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
14 Yahweh said to Moses, “Pharaoh's heart is hard, and he refuses to let the people go.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 Go to Pharaoh in the morning when he goes out to the water. Stand on the riverbank to meet him, and take in your hand the staff that had turned into a snake.
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 Say to him, 'Yahweh, the God of the Hebrews, has sent me to you to say, “Let my people go, so that they may worship me in the wilderness. Until now you have not listened.”
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 Yahweh says this: “By this you will know that I am Yahweh. I am going to strike the water of the Nile River with the staff that is in my hand, and the river will be turned to blood.
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 The fish that are in the river will die, and the river will stink. The Egyptians will not be able to drink water from the river.”'”
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 Then Yahweh said to Moses, “Say to Aaron, 'Take your staff and reach out with your hand over the waters of Egypt, and over their rivers, streams, pools, and all their ponds, so that their water may become blood. Do this so that there will be blood throughout all the land of Egypt, even in containers of wood and stone.'”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 Moses and Aaron did as Yahweh commanded. Aaron raised the staff and struck the water in the river, in the sight of Pharaoh and his servants. All the water in the river turned to blood.
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 The fish in the river died, and the river began to stink. The Egyptians could not drink water from the river, and the blood was everywhere in the land of Egypt.
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 But the magicians of Egypt did the same thing with their magic. So Pharaoh's heart was hardened, and he refused to listen to Moses and Aaron, just as Yahweh had said would happen.
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
23 Then Pharaoh turned and went into his house. He did not even pay attention to this.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 All the Egyptians dug around the river for water to drink, but they could not drink the water of the river itself.
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
25 Seven days passed after Yahweh had attacked the river.
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.