< Exodus 23 >
1 You must not give a false report about anyone. Do not join with a wicked man to be a dishonest witness.
“Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada kuma ku haɗa baki da mugayen mutane har da ku zama munafukai ta wurin ba da shaidar ƙarya.
2 You must not follow a crowd to do evil, nor may you bear witness while siding with the crowd in order to pervert justice.
“Kada ku yi abin da ba daidai ba, don galibin mutane suna yin haka. Sa’ad da kuke ba da shaida a gaban shari’a, kada ku ba da shaidar ƙarya a kauce wa gaskiya don ku faranta wa taron jama’a rai.
3 You must not show favoritism to a poor man in his lawsuit.
Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari’a.
4 If you meet your enemy's ox or his donkey going astray, you must bring it back to him.
“In ka ga saniyar abokin gābanka, ko jakinsa ya ɓace, ka yi ƙoƙari ka mai da shi wurinsa.
5 If you see the donkey of someone who hates you fallen to the ground under its load, you must not leave that person. You must surely help him with his donkey.
In ka ga jakin wani maƙiyinka ya fāɗi a ƙarƙashin kayan da ya ɗauka, kada ka bar shi can, ka yi ƙoƙari ka taimake shi.
6 Do not thrust aside justice for your poor in his lawsuit.
“Kada ku kāsa yin adalci ga matalauci a wurin shari’a.
7 Do not join others in making false accusations, and do not kill the innocent or righteous, for I will not acquit the wicked.
Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi tare da mai adalci, gama ba zan bar mugun yă tafi haka kawai ba.
8 Never take a bribe, for a bribe blinds those who see, and perverts honest people's words.
“Kada ka karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta waɗanda suke gani, yakan kuma karkatar da maganar masu adalci.
9 You must not oppress a foreigner, since you know the life of a foreigner, for you were foreigners in the land of Egypt.
“Kada ka zalunci baƙo, ku kanku kun san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a Masar.
10 For six years you will sow seed on your land and gather in its produce.
“Shekara shida za ku nome gonakinku ku girbe amfanin gonar,
11 But in the seventh year you will leave it unplowed and fallow, so that the poor among your people may eat. What they leave, the wild animals will eat. You will do the same with your vineyards and olive orchards.
amma a shekara ta bakwai za ku bar ƙasa tă huta. Sa’an nan matalautan da suke cikinku za su sami abinci daga cikinta, namun jeji kuma za su ci abin da aka bari. Ku yi haka da gonakinku na inabi, da na itatuwan zaitun.
12 During six days you will do your work, but on the seventh day you must rest. Do this so that your ox and your donkey may have rest, and so that your female slave's son and any foreigner may rest and be refreshed.
“Kwana shida za ku yi aikinku, amma a rana ta bakwai, kada ku yi aiki, saboda saniyarku da jakinku su huta, haka kuma bawan da aka haifa a gidanku, da kuma baƙon da yake a cikinku yă wartsake.
13 Pay attention to everything that I have said to you. Do not mention the names of other gods, nor let their names be heard from your mouth.
“Ku mai da hankali, ku yi biyayya da duk abin da na faɗa muku. Kada ku kira sunaye waɗansu alloli; kada a ji su a bakinku.
14 You must travel to hold a festival for me three times every year.
“Sau uku a shekara za ku yi mini biki.
15 You are to observe the Festival of Unleavened Bread. As I commanded you, you will eat unleavened bread for seven days. At that time, you will appear before me in the month of Aviv, which is fixed for this purpose. It was in this month that you came out from Egypt. But you must not appear before me empty-handed.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a lokacin da aka ayana a watan Abib, gama a watan ne kuka fito daga Masar. “Kada wani yă zo a gabana hannu wofi.
16 You must observe the Festival of Harvest, the firstfruits of your labors when you sowed seed in the fields. Also you must observe the Festival of Ingathering at the end of the year, when you gather in your produce from the fields.
“Ku yi Bikin Girbi da nunan fari na amfanin shuke-shuken gonarku. “Ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa’ad da kuka tattara amfani daga gonarku.
17 All your males must appear before the Lord Yahweh three times every year.
“Sau uku a shekara, maza duka za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka.
18 You must not offer the blood from sacrifices made to me with bread containing yeast. The fat from the sacrifices at my festivals must not remain all night until the morning.
“Kada ku miƙa mini hadayar jini tare da wani abu mai yisti. “Ba za a bar kitsen bikin hadayata yă kwana ba.
19 You must bring the choicest firstfruits from your land into my house, the house of Yahweh your God. You must not boil a young goat in its mother's milk.
“Dole ne ku kawo mafi kyau daga nunan fari na gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.
20 I am going to send an angel before you to guard you on the way, and to bring you to the place that I have prepared.
“Ga shi, zan aika mala’ika a gabanku, yă tsare ku a tafiyarku, yă kuma kawo ku wurin da na shirya.
21 Be attentive to him and obey him. Do not provoke him, for he will not pardon your transgressions. My name is on him.
Ku saurare shi, ku kuma kasa kunne ga abin da yake faɗa. Kada ku yi masa tawaye; ba zai gafarta tawayenku ba, gama shi wakilina ne.
22 If you indeed obey his voice and do everything that I tell you, then I will be an enemy to your enemies and an adversary to your adversaries.
In kun kasa kunne sosai ga abin da yake faɗi, kuka kuma yi abin da na faɗa, zan zama magabci ga abokan gābanku, zan kuma yi hamayya da abokan hamayyanku.
23 My angel will go before you and bring you to the Amorites, Hittites, Perizzites, Canaanites, Hivites, and the Jebusites. I will destroy them.
Mala’ikana zai sha gabanku, yă kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan’aniyawa, da Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa, zan kuma kawar da su.
24 You must not bow down to their gods, worship them, or do as they do. Instead, you must completely overthrow them and smash their stone pillars in pieces.
Kada ku durƙusa wa allolinsu, ko ku yi musu sujada, ko kuma ku bi al’adunsu. Za ku hallaka dukan allolinsu, ku kuma farfasa keɓaɓɓun duwatsunsu.
25 You must worship Yahweh your God, and he will bless your bread and water. I will remove sickness from among you.
Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, albarkansa kuwa za tă kasance a kan abincinku da ruwan shanku. Zan ɗauke cuta daga cikinku.
26 No woman will be barren or will miscarry her young in your land. I will give you long lives.
A ƙasarku, mace ba za tă yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.
27 I will send fear of myself on those into whose land you advance. I will kill all the people whom you meet. I will make all your enemies turn their backs to you in fright.
“Zan aiki razanata a gabanku, in kuma sa ruɗami a cikin kowace al’ummar da za ku sadu da ita. Zan sa duk abokan gābanku su juye da baya, su gudu.
28 I will send hornets before you that will drive out the Hivites, Canaanites, and the Hittites from before you.
Zan aiki rina a gabanku, su kori Hiwiyawa, Kan’aniyawa da kuma Hittiyawa.
29 I will not drive them out from before you in one year, or the land would become abandoned, and the wild animals would become too many for you.
Amma ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar tă zama kufai har namun jeji su fi ƙarfinku.
30 Instead, I will drive them out little by little from before you until you become fruitful and inherit the land.
Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku yă kai yadda za ku mallaki ƙasar.
31 I will fix your borders from the Sea of Reeds to the Sea of the Philistines, and from the wilderness to the Euphrates River. I will give you victory over the land's inhabitants. You will drive them out before yourselves.
“Zan kafa iyakokinku daga Jan Teku zuwa Bahar Rum, daga hamada kuma zuwa Kogi. Zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kuwa kore su daga gabanku.
32 You must not make a covenant with them or with their gods.
Kada ku ƙulla yarjejjeniya da su, ko da allolinsu.
33 They must not live in your land, or they would make you sin against me. If you worship their gods, this will surely become a trap for you.'”
Kada ku bari su zauna a cikin ƙasarku, in har kuka bar su, za su ɓata ku da zunubinsu na bautar allolinsu, har zai yă zama muku tarko.”