< Amos 7 >

1 This is what the Lord Yahweh showed me. Look, he formed a locust swarm when the spring crop began to come up, and, look, it was the late crop after the king's harvest.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
2 When they finished eating the vegetation of the land, then I said, “Lord Yahweh, please forgive; how will Jacob survive? For he is so small.”
Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
3 Yahweh relented concerning this. “It will not happen,” he said.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
4 This is what the Lord Yahweh showed me: Look, the Lord Yahweh called on fire to judge. It dried the vast, deep water under the earth and would have devoured the land, also.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
5 But I said, “Lord Yahweh, please stop; how will Jacob survive? For he is so small.”
Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
6 Yahweh relented concerning this, “This also will not happen,” said the Lord Yahweh.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
7 This is what he showed me: Look, the Lord stood beside a wall, with a plumb line in his hand.
Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
8 Yahweh said to me, “Amos, what do you see?” I said, “A plumb line.” Then the Lord said, “Look, I will put a plumb line among my people Israel. I will spare them no longer.
Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
9 The high places of Isaac will be destroyed, the sanctuaries of Israel will be ruined, and I will rise against the house of Jeroboam with the sword.”
“Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
10 Then Amaziah, the priest of Bethel, sent a message to Jeroboam, king of Israel: “Amos has conspired against you in the middle of the house of Israel. The land cannot bear all his words.
Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
11 For this is what Amos said, 'Jeroboam will die by the sword, and Israel will surely go into exile away from his land.'”
Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
12 Amaziah said to Amos, “Seer, go, run back to the land of Judah, and there eat bread and prophesy.
Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
13 But do not prophesy anymore here at Bethel, for it is the king's sanctuary and a royal house.”
Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
14 Then Amos said to Amaziah, “I am not a prophet nor a prophet's son. I am a herdsman, and I take care of sycamore fig trees.
Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
15 But Yahweh took me from tending the flock and said to me, 'Go, prophesy to my people Israel.'
Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
16 Now hear the word of Yahweh. You say, 'Do not prophesy against Israel, and do not speak against the house of Isaac.'
Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
17 Therefore this is what Yahweh says, 'Your wife will be a prostitute in the city; your sons and your daughters will fall by the sword; your land will be measured and divided up; you will die in an unclean land, and Israel will surely go into exile from his land.'”
“Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”

< Amos 7 >