< 2 Samuel 3 >
1 Now there was a long war between the house of Saul and the house of David. David grew stronger and stronger, but the house of Saul grew weaker and weaker.
Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
2 Sons were born to David in Hebron. His firstborn was Amnon, by Ahinoam from Jezreel.
An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
3 His second son, Kileab, was born to Abigail, the widow of Nabal from Carmel. The third, Absalom, was son of Maacah, daughter of Talmai, king of Geshur.
na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
4 David's fourth son, Adonijah, was the son of Haggith. His fifth son was Shephatiah son of Abital,
na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
5 and the sixth, Ithream, was the son of David's wife Eglah. These sons were born to David in Hebron.
na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
6 It came about during the war between the house of Saul and the house of David that Abner made himself strong in the house of Saul.
Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
7 Saul had a concubine whose name was Rizpah, the daughter of Aiah. Ishbosheth said to Abner, “Why have you slept with my father's concubine?”
To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
8 Then Abner was very angry at the words of Ishbosheth and said, “Am I a dog's head that belongs to Judah? Today I am showing faithfulness to the house of Saul, your father, to his brothers, and to his friends, by not delivering you into the hand of David. But now you accuse me of an offense concerning this woman?
Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
9 May God do so to me, Abner, and more also, if I do not do for David as Yahweh has sworn to him,
Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
10 to transfer the kingdom from the house of Saul and set up the throne of David over Israel and over Judah, from Dan to Beersheba.”
Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
11 Ishbosheth could not answer Abner another word, because he feared him.
Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
12 Then Abner sent messengers to David to speak for him saying, “Whose land is this? Make a covenant with me, and you will see that my hand is with you, to bring all Israel to you.”
Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
13 David answered, “Good, I will make a covenant with you. But one thing I require from you is that you cannot see my face unless you first bring Michal, Saul's daughter, when you come to see me.”
Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
14 Then David sent messengers to Ishbosheth, Saul's son, saying, “Give me my wife Michal, for whom I paid a price of one hundred Philistine foreskins.”
Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
15 So Ishbosheth sent for Michal and took her from her husband, Paltiel son of Laish.
Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
16 Her husband went with her, weeping as he went, and followed her to Bahurim. Then Abner said to him, “Return home now.” So he returned.
Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
17 Abner spoke with the elders of Israel saying, “In the past you were trying to have David be king over you.
Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
18 Now do it. For Yahweh has spoken of David saying, 'By the hand of my servant David I will save my people Israel from the hand of the Philistines and from the hand of all their enemies.'”
To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
19 Abner also spoke personally to the people of Benjamin. Then Abner went also to speak with David in Hebron to explain everything that Israel and the whole house of Benjamin desired to accomplish.
Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
20 When Abner and twenty of his men arrived in Hebron to see David, David had a feast prepared for them.
Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
21 Abner explained to David, “I will arise and gather all Israel to you, my master the king, so that they may make a covenant with you, so that you may reign over all that you desire.” So David sent Abner away, and Abner left in peace.
Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
22 Then the soldiers of David and Joab came from a raid and brought much plunder with them. But Abner was not with David in Hebron. David had sent him away, and Abner had left in peace.
Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
23 When Joab and all the army with him arrived, they told Joab, “Abner son of Ner came to the king, and the king has sent him away, and Abner left in peace.”
Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
24 Then Joab came to the king and said, “What have you done? Look, Abner came to you! Why have you sent him away, and he is gone?
Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
25 Do you not know that Abner son of Ner came to deceive you and to discover your plans and learn everything you are doing?”
Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
26 When Joab left David, he sent messengers after Abner, and they brought him back from the well of Sirah, but David did not know this.
Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
27 When Abner returned to Hebron, Joab took him aside in the middle of the gate to speak with him quietly. There Joab stabbed him in the stomach and killed him. In this way, Joab avenged the blood of Asahel his brother.
To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
28 When David heard about this he said, “I and my kingdom are innocent before Yahweh forever regarding the blood of Abner son of Ner.
Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
29 Let the guilt of Abner's death fall on the head of Joab and on all his father's house. May there never fail to be in the family of Joab someone who has a flowing sore or skin disease or who is lame and must walk with a staff or who is killed by the sword or who goes without food.”
Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
30 So Joab and Abishai his brother killed Abner, because he had killed their brother Asahel at Gibeon in battle.
(Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
31 David said to Joab and to all the people who were with him, “Tear your clothes, put on sackcloth, and mourn before Abner's body.” Now King David walked behind the body in the funeral procession.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
32 They buried Abner in Hebron. The king wept and cried loudly at the tomb of Abner, and all the people also wept.
Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
33 The king lamented for Abner and sang, “Should Abner die as a fool dies?
Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
34 Your hands were not bound. Your feet were not shackled. As a man falls before the sons of injustice, so you have fallen.” Once more all the people wept over him.
Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
35 All the people came to make David eat while it was still day, but David swore, “May God do so to me, and more also, if I taste bread or anything else before the sun goes down.”
Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
36 All the people took notice of David's grief, and it pleased them, as whatever the king did pleased them.
Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
37 So all the people and all Israel understood that day that it was not the king's desire to kill Abner son of Ner.
Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
38 The king said to his servants, “Do you not know that a prince and a great man has fallen this day in Israel?
Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
39 Now I am weak today, though I am an anointed king. These men, the sons of Zeruiah, are too brutal for me. May Yahweh repay the evildoer by punishing him for his wickedness, as he deserves.”
A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”