< 2 Samuel 23 >

1 Now these are the last words of David— David son of Jesse, the man who was highly honored, the one anointed by the God of Jacob, the sweet psalmist of Israel.
Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
2 “The Spirit of Yahweh spoke by me, and his word was on my tongue.
“Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
3 The God of Israel spoke, the Rock of Israel said to me, 'The one who rules righteously over men, who rules in the fear of God.
Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
4 He will be like the morning light when the sun rises, a morning without clouds, when the tender grass springs up from the earth through bright sunshine after rain.
yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
5 Indeed, is my family not like this before God? Has he not made an everlasting covenant with me, ordered and sure in every way? Does he not increase my salvation and fulfill my every desire?
“Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
6 But the worthless will all be like thorns to be thrown away, because they cannot be gathered by one's hands.
Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
7 The man who touches them must use an iron tool or the shaft of a spear. They must be burned up where they lie.'”
Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
8 These are the names of David's mighty men: Jeshbaal the Hachmonite was the leader of the mighty men. He killed eight hundred men on one occasion.
Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
9 After him was Eleazar son of Dodai the Ahohite, one of the three mighty men. He was with David when they taunted the Philistines who had gathered together to do battle, and when the men of Israel had retreated.
Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
10 Eleazar stood and fought the Philistines until his hand became weary and his hand stiffened to the grip of his sword. Yahweh brought about a great victory that day. The army returned after Eleazar, only to strip the bodies.
amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
11 After him was Shammah son of Agee, a Hararite. The Philistines gathered together where there was a field of lentils, and the army fled from them.
Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
12 But Shammah stood in the middle of the field and defended it. He killed the Philistines, and Yahweh brought about a great victory.
Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
13 Three of the thirty soldiers went down to David at harvest time, to the cave of Adullam. The army of the Philistines was camped in the Valley of Rephaim.
A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
14 At that time David was in his stronghold, a cave, while the Philistines had established at Bethlehem.
Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
15 David was longing for water and said, “If only someone would give me water to drink from the well at Bethlehem, the well that is by the gate!”
Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
16 So these three mighty men broke through the army of the Philistines and drew water out of the well of Bethlehem, the well at the gate. They took the water and brought it to David, but he refused to drink it. Instead, he poured it out to Yahweh.
Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
17 Then he said, “Yahweh, far be it from me, that I should do this. Should I drink the blood of men who have risked their lives?” So he refused to drink it. These things were done by the three mighty.
Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
18 Abishai, brother of Joab and son of Zeruiah, was captain over the three. He once fought with his spear against three hundred men and killed them. He was often mentioned along with the three soldiers.
Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
19 Was he not even more famous than the three? He was made their captain. However, his fame did not equal the fame of the three most famous soldiers.
Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
20 Benaiah from Kabzeel was the son of Jehoiada; he was a strong man who did mighty feats. He killed the two sons of Ariel of Moab. He also went down into a pit and killed a lion while it was snowing.
Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
21 Then he killed a very large Egyptian man. The Egyptian had a spear in his hand, but Benaiah fought against him with only a staff. He seized the spear out of the Egyptian's hand and then killed him with his own spear.
Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
22 Benaiah son of Jehoiada did these feats, and he was named alongside the three mighty men.
Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
23 He was more highly regarded than the thirty soldiers in general, but he was not regarded quite as highly as the three mighty men. Yet David put him in charge of his bodyguard.
Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
24 The thirty included the following men: Asahel brother of Joab, Elhanan son of Dodo from Bethlehem,
Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
25 Shammah the Harodite, Elika the Harodite,
Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
26 Helez the Paltite, Ira son of Ikkesh the Tekoite,
Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
27 Abiezer the Anathothite, Sibbekai the Hushathite,
Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
28 Zalmon the Ahohite, Maharai the Netophathite;
Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
29 Heleb son of Baanah, the Netophathite, Ithai son of Ribai from Gibeah of the Benjamites,
Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
30 Benaiah the Pirathonite, Hiddai of the valleys of Gaash.
Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
31 Abi-Albon the Arbathite, Azmaveth the Barhumite,
Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
32 Eliahba the Shaalbonite, the sons of Jashen, Jonathan son of Shammah the Hararite;
Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
33 Ahiam son of Sharar the Hararite,
ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
34 Eliphelet son of Ahasbai the Maakathite, Eliam son of Ahithophel the Gilonite,
Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
35 Hezro the Carmelite, Paarai the Arbite,
Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
36 Igal son of Nathan from Zobah, Bani from the tribe of Gad,
Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
37 Zelek the Ammonite, Naharai the Beerothite, armor bearer to Joab son of Zeruiah,
Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
38 Ira the Ithrite, Gareb the Ithrite,
Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
39 Uriah the Hittite—thirty-seven in all.
da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.

< 2 Samuel 23 >