< 2 Chronicles 23 >
1 In the seventh year, Jehoiada showed his strength and entered into a covenant with the commanders of hundreds, Azariah son of Jeroham, Ishmael son of Jehohanan, Azariah son of Obed, Maaseiah son of Adaiah, and Elishaphat son of Zichri.
A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
2 They went about in Judah and gathered the Levites from all the cities of Judah, as well as the heads of the ancestral houses of Israel, and they came to Jerusalem.
Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
3 All the assembly made a covenant with the king in the house of God. Jehoiada said to them, “See, the king's son will reign, as Yahweh has said concerning the descendants of David.
dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
4 This is what you must do: A third of you priests and Levites who come to serve on the Sabbath will be guards at the doors.
Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
5 Another third will be at the king's house, and the other third will be at the Foundation Gate. All the people will be in the courtyard of the house of Yahweh.
kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
6 Allow no one to come into the house of Yahweh, except for the priests and the Levites who are serving. They may enter because they are consecrated. But all the other people must obey the commands of Yahweh.
Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
7 The Levites must surround the king on all sides, every man with his weapons in his hand. Whoever comes into the house, let him be killed. Stay with the king when he comes in and when he goes out.”
Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
8 So the Levites and all Judah served in every way in the manner in which Jehoiada the priest commanded. Each one took his men, those who were to come in to serve on the Sabbath, and those who were to leave off serving on the Sabbath, for Jehoiada the priest had not dismissed any of their divisions.
Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
9 Then Jehoiada the priest brought to the commanders spears and small and large shields that had been King David's that were in the house of God.
Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
10 Jehoiada placed all the soldiers, each man with his weapon in his hand, from the right side of the temple to the left side of the temple, along by the altar and the temple, surrounding the king.
Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
11 Then they brought out the king's son, put the crown on him, and gave him the covenant decrees. Then they made him king, and Jehoiada and his sons anointed him. Then they said, “Long live the king.”
Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
12 When Athaliah heard the noise of the people running and praising the king, she came to the people in the house of Yahweh,
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
13 and she looked, and, behold, the king was standing by his pillar at the entrance, and the commanders and the trumpeters were by the king. All the people of the land were rejoicing and blowing trumpets, and the singers were playing musical instruments and leading the singing of praise. Then Athaliah tore her clothes and shouted, “Treason! Treason!”
Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
14 Then Jehoiada the priest brought out the commanders of hundreds who were over the army and said to them, “Bring her out between the ranks; anyone who follows her, let him be killed with the sword.” For the priest had said, “Do not kill her in the house of Yahweh.”
Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
15 So they seized her as she went into the entrance of the Horse Gate of the king's house, and there they killed her.
Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
16 Then Jehoiada made a covenant between himself, all the people, and the king, that they should be Yahweh's people.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
17 So all the people went to the house of Baal and tore it down. They smashed Baal's altars and his images to pieces, and they killed Mattan, the priest of Baal, in front of those altars.
Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
18 Jehoiada appointed officers for the house of Yahweh under the hand of the priests, who were Levites, whom David had assigned to the house of Yahweh, to offer the burnt offerings to Yahweh, as it was written in the law of Moses, together with rejoicing and singing, as David had given direction.
Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
19 Jehoiada set guards at the gates of the house of Yahweh, so that no one that was unclean in any way should enter.
Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
20 Jehoiada took with him the commanders of hundreds, the noblemen, the governors of the people, and all the people of the land. He brought down the king from the house of Yahweh; the people came through the Upper Gate to the king's house and sat the king on the throne of the kingdom.
Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
21 So all the people of the land rejoiced, and the city was quiet. As for Athaliah, they had killed her with the sword.
sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.