< 2 Chronicles 21 >
1 Jehoshaphat slept with his ancestors and was buried with them in the city of David; Jehoram, his son, became king in his place.
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Jehoram had brothers, sons of Jehoshaphat: Azariah, Jehiel, Zechariah, Azariahu, Michael, and Shephatiah. All these were sons of Jehoshaphat, king of Israel.
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
3 Their father had given them large gifts of silver, gold, and other precious things, and also fortified cities in Judah, but he gave the kingdom to Jehoram.
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
4 Now when Jehoram had risen up over his father's kingdom and had firmly established himself as king, he killed all his brothers with the sword, and also various other leaders of Israel.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
5 Jehoram was thirty-two years old when he began to reign, and he reigned for eight years in Jerusalem.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
6 He walked in the ways of the kings of Israel, as the house of Ahab was doing, for he had Ahab's daughter as his wife, and he did what was evil in the sight of Yahweh.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
7 However, Yahweh did not wish to destroy the house of David, because of the covenant that he had made with David; he had promised that he would always give life to him and his descendants.
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
8 In Jehoram's days, Edom revolted from the control of Judah, and they set a king over themselves.
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
9 Then Jehoram crossed over with his commanders and all his chariots. It was night when he rose up and fought against the Edomites who had surrounded him and his chariot commanders.
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
10 So Edom has been in rebellion from the control of Judah to this present day. Libnah also revolted at the same time from his control, because Jehoram had forsaken Yahweh, the God of his ancestors.
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
11 In addition, Jehoram had also built high places in the mountains of Judah and he made the inhabitants of Jerusalem to live like prostitutes, and he led Judah astray.
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
12 A letter from the prophet Elijah came to Jehoram. It said, “This is what Yahweh, the God of David, your ancestor, says: Because you have not walked in the ways of Jehoshaphat, your father, nor in the ways of Asa, king of Judah,
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
13 but have walked in the ways of the kings of Israel, and have made Judah and the inhabitants of Jerusalem to act like a prostitute, as the house of Ahab did—and because you have also killed your brothers in your father's family, men who were better than yourself—
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
14 see, Yahweh will strike with a great plague your people, your children, your wives, and all your possessions.
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
15 You yourself will have much sickness because of a disease in your intestines, until your intestines fall out because of the sickness, day after day.”
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
16 Yahweh stirred up against Jehoram the spirit of the Philistines and of the Arabians who were near the Cushites.
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
17 They attacked Judah, invaded it, and carried away all the wealth that was found in the king's house. They also carried away his sons and his wives. No son was left to him except Jehoahaz, his youngest son.
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
18 After all this, Yahweh struck him in his intestines with an incurable disease.
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
19 It came about in due time, at the end of two years, that his intestines fell out because of his sickness, and that he died of severe disease. His people made no fire in his honor as they had done for his ancestors.
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
20 He had begun to reign when he was thirty-two years old; he reigned in Jerusalem for eight years, and when he departed no one mourned him. They buried him in the city of David, but not in the royal tombs.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.