< 2 Chronicles 16 >
1 In the thirty-sixth year of Asa's reign, Baasha, king of Israel, acted aggressively against Judah and built up Ramah, so that he might not allow anyone to leave or enter into the land of Asa, king of Judah.
A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
2 Then Asa brought the silver and gold out of the storerooms in the house of Yahweh and of the king's house, and sent it to Ben Hadad king of Aram, who lived in Damascus. He said,
Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
3 “Let there be a covenant between me and you, as there was between my father and your father. Look, I have sent to you silver and gold. Break your covenant with Baasha, king of Israel, so that he may leave me alone.”
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
4 Ben Hadad listened to King Asa and sent the commanders of his armies against the cities of Israel. They attacked Ijon, Dan, Abel Maim, and all the storage cities of Naphtali.
Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
5 It came about that when Baasha heard this, he stopped building up Ramah, and let his work cease.
Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
6 Then Asa the king took all Judah with him. They carried away the stones and timbers of Ramah with which Baasha had been building up the city. Then King Asa used that building material to build up Geba and Mizpah.
Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
7 At that time Hanani the seer went to Asa, king of Judah, and said to him, “Because you have relied on the king of Aram, and have not relied on Yahweh your God, the army of the king of Aram has escaped out of your hand.
A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
8 Were not the Cushites and the Libyans a huge army, with very many chariots and horsemen? Yet, because you relied on Yahweh, he gave you victory over them.
Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
9 For the eyes of Yahweh run everywhere throughout the whole earth, so that he might show himself strong on behalf of those whose hearts are perfect toward him. But you have acted foolishly in this matter. From now on, you will have war.”
Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
10 Then Asa was angry with the seer; he put him into prison, for he was angry with him over this matter. At the same time, Asa oppressed some of the people.
Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
11 Behold, the deeds of Asa, from first to last, behold, they are written in the book of the kings of Judah and Israel.
Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
12 In the thirty-ninth year of his reign, Asa was afflicted with a disease in his feet. Though his disease was very severe, he did not seek help from Yahweh, but only from the physicians.
A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
13 So Asa slept with his ancestors, dying in the forty-first year of his reign.
Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
14 They buried him in his own tomb, which he had dug out for himself in the city of David. They laid him on a bier that was filled with sweet odors and various kinds of spices prepared by skilled perfumers. Then they made a very great fire in his honor.
Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.