< Luke 7 >
1 When he had ended all his sainges in the audience of the people he entred into Capernau
Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
2 And a certayne Centurions seruaunte was sicke and redy to dye whom he made moche of.
A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
3 And when he hearde of Iesu he sent vnto him the elders of the Iewes besechinge him yt he wolde come and heale his servaunt.
Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
4 And they came to Iesus and besought him instantly sayinge: He is worthi that thou shuldest do this for him.
Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
5 For he loveth oure nacion and hath bilt vs a sinagoge
gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
6 And Iesus went with them. And when he was not farre fro the housse the Centurio sent frendes to him sayinge vnto him: Lorde trouble not thy silfe: for I am not worthy yt thou shuldest enter vnder my roffe.
Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
7 Wherfore I thought not my silfe worthy to come vnto the: but saye the worde and my servaunt shalbe whoole.
Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
8 For I lyke wyse am a man vnder power and have vnder me soudiers and I saye vnto won goo: and he goeth. And to another come: and he cometh. And to my servaunt do this: and he doeth it.
Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
9 When Iesus herde this he merveyled at him and turned him about and sayd to the people that folowed him: I saye vnto you I have not founde so greate faith noo not in Israel.
Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
10 And they yt were sent turned backe home agayne and founde the servaunt that was sicke whoole.
Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
11 And it fortuned after that that he went into a cite called Naim and many of his disciples went wt him and moche people.
Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
12 When he came nye to the gate of the cite: beholde ther was a deed man caried out which was ye only sonne of his mother and she was a widowe and moche people of the cite was with her.
Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
13 And when ye lorde sawe her he had compassion on her and sayde vnto her: wepe not.
Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
14 And he went and touched the coffyn and they yt bare him stode still. And he sayde: Yonge man I saye vnto the aryse.
Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
15 And ye deed sate vp and beganne to speake. And he delyvered him to his mother.
Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
16 And ther ca a feare on the all. And they glorified god sayinge: a greate prophet is rysen amoge vs and god hath visited his people
Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
17 And this rumor of him wet forthe throughout all Iurie and thorowout all the regions which lye rounde about.
Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
18 And ye disciples of Iohn shewed him of all these thinges.
Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
19 And Iohn called vnto him. ii. of his disciples and sent the to Iesus sayinge: Arte thou he that shall come: or shall we loke for another?
ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
20 When the men were come vnto him they sayde: Iohn baptiste sent vs vnto ye sayinge: Arte thou he that shall come: or shall we wayte for another?
Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
21 And at yt same tyme he cured many of their infirmites and plages and of evyll spretes and vnto many that were blynde he gave sight
A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
22 And Iesus answered and sayd vnto them: Goo youre wayes and shewe Iohn what thinges ye have sene and harde: how yt the blynde se the halt goo the lepers are clensed the deafe heare the deed aryse to the poore is the glad tydinges preached
Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
23 and happy is he that is not offended by me.
Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
24 When ye messengers of Iohn were departed he began to speake vnto ye people of Iohn What wet ye oute into ye wildernes for to se? went ye to se arede shaken wt ye wynde?
Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
25 But what went ye out for tose? A ma clothed in soofte rayment? Beholde they which are gorgeously apparelled and lyve delicatly are in kynges courtes.
In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
26 But what went ye forth to se? A prophete? Ye I saye to you and moare then a prophete
Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
27 This is he of who it is wrytte: Beholde I sende my messenger before thy face to prepare thy waye before the.
Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
28 For I saye vnto you: a greater prophete then Iohn amoge wemes chyldre is ther none. Neverthelesse one yt is lesse in ye kyngdo of god is greater the he
Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
29 And all the people that hearde and the publicans iustified God and were baptised with the baptim of Iohn.
(Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
30 But the pharises and scribes despised ye counsell of god agaynst them selves and were not baptised of him.
Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
31 And ye lorde sayd: Wher vnto shall I lyke the men of this generacion and what thinge are they lyke?
Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
32 They are lyke vnto chyldre sittynge in ye market place and cryinge one to another and sayinge: We have pyped vnto you and ye hahave not daunsed: we have mourned to you and ye have not wept.
Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
33 For Iohn baptist cam nether eatynge breed ner drinkynge wyne and ye saye: he hath the devyll.
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
34 The sonne of man is come and eateth and drinketh and ye saye: beholde a man which is a glotton and a drinker of wyne a frende of publicans and synners.
Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
35 Yet is wysdome iustified of all her chyldren.
Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
36 And one of the pharises desyred him that he wolde eate with him. And he went into ye pharises housse and sate doune to meate.
To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
37 And beholde a woman in that cite which was a synner assone as she knewe that. Iesus sate at meate in the pharises housse she brought an alablaster boxe of oyntmet
Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
38 and she stode at his fete behynde him wepynge and beganne to wesshe his fete with teares and dyd wipe the with the heares of her heed and kyssed his fete and anoynted them with oyntment.
ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
39 When the pharise which bade him sawe that he spake with in him sylfe sayinge: If this man were a prophete he wolde surely have knowen who and what maner woman this is which toucheth him for she is a synner.
Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
40 And Iesus answered and sayde vnto him: Simon I have some what to saye vnto ye. And he sayd master saye on.
Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
41 There was a certayne lender which had two detters ye one ought five hondred pence and the other fyfty.
Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
42 When they had nothinge to paye he forgave the boothe. Which of them tell me will love him moost?
Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
43 Simon answered and sayde: I suppose that he to whom he forgave moost. And he sayde vnto him: Thou hast truly iudged.
Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
44 And he turned to the woman and sayde vnto Simon: Seist thou this woman? I entred into thy housse and thou gavest me noo water to my fete but she hath wesshed my fete with teares and wiped the with the heeres of her heed.
Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
45 Thou gavest me no kysse: but she sence ye tyme I came in hath not ceased to kysse my fete
Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
46 Myne heed wt oyle thou dydest not anoynte: but she hath annoynted my fete wt oyntmet.
Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
47 Wherefore I saye vnto the: many synnes are forgeve her for she loved moche. To whom lesse is forgeven the same doeth lesse love.
“Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
48 And he sayde vnto her thy synnes are forgeven ye
Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
49 And they yt sate at meate with him beganne to saye within them selves: Who is this which forgeveth synnes also?
Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
50 And he sayde to ye woman: Thy faith hath saved the Goo in peace.
Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”