< Genesis 43 >
1 And the derth waxed sore in the lande.
A yanzu, yunwa ta yi tsanani a ƙasar.
2 And when they had eate vp that corne which they brought out of the lande of Egipte their father sayde vnto them: goo agayne and by vs a litle food.
Saboda haka sa’ad da suka cinye dukan hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ƙarin abinci.”
3 Than sayde Iuda vnto him: the man dyd testifie vnto vs saynge: loke that ye see not my face excepte youre brother be with you.
Amma Yahuda ya ce masa, “Mutumin ya gargaɗe mu sosai cewa, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai in ɗan’uwanku yana tare da ku.’
4 Therfore yf thou wilt sende oure brother with vs we wyll goo and bye the food.
In za ka aika da ɗan’uwanmu tare da mu, za mu gangara mu sayo maka abinci.
5 But yf thou wylt not sende him we wyll not goo: for the man sayde vnto vs: loke that ye see not my face excepte youre brother be with you.
Amma in ba za ka aika da shi ba, ba za mu gangara ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai ko in ɗan’uwanku yana tare da ku.’”
6 And Israell sayde: wherfore delt ye so cruelly with me as to tell the man that ye had yet another brother?
Isra’ila ya yi tambaya, “Me ya sa kuka kawo wannan damuwa a kaina ta wurin faɗa wa mutumin cewa kuna da wani ɗan’uwa?”
7 And they sayde: The man asked vs of oure kynred saynge: is youre father yet alyue? haue ye not another brother? And we tolde him acordynge to these wordes. How cowd we knowe that he wolde byd vs brynge oure brother downe with vs?
Suka amsa, “Mutumin ya yi mana tambaya sosai game da kanmu da iyalinmu. Ya tambaye mu, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna da wani ɗan’uwa?’ Mu dai mun amsa tambayoyinsa ne. Ta yaya za mu sani zai ce, ‘Ku kawo ɗan’uwanku a nan’?”
8 Than sayde Iuda vnto Israell his father: Send the lad with me and we wyll ryse and goo that we maye lyue and not dye: both we thou and also oure childern.
Sa’an nan Yahuda ya ce wa Isra’ila mahaifinsa, “Ka aika saurayin tare da ni za mu kuwa tafi nan da nan, saboda mu da’ya’yanmu mu rayu, kada mu mutu.
9 I wilbe suertie for him and of my handes requyre him. Yf I brynge him not to the and sett him before thine eyes than let me bere the blame for euer.
Ni kaina zan tabbatar da lafiyarsa; na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. In ban dawo da shi gare ka, in sa shi nan a gabanka ba, zan ɗauki laifin a gabanka dukan kwanakina.
10 For except we had made this tarieg: by this we had bene there twyse and come agayne.
Ai, da ba mun jinkirta ba, da mun komo har sau biyu.”
11 Than their father Israel sayde vnto the Yf it must nedes be so now: than do thus take of the best frutes of the lande in youre vesselles and brynge the man a present a curtesie bawlme and a curtesie of hony spyces and myrre dates and almondes.
Sa’an nan mahaifinsu Isra’ila ya ce musu, “In dole ne a yi haka, to, sai ku yi. Ku sa waɗansu amfani mafi kyau na ƙasar a buhunanku, ku ɗauka zuwa wurin mutumin a matsayin kyauta, da ɗan man ƙanshi na shafawa, da kuma’yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta da kuma almon.
12 And take as moch money more with you. And the money that was brought agayne in youre sackes take it agayne with you in youre handes peraduenture it was some ouersyghte.
Ku ɗauki ninki biyu na yawan azurfa tare da ku, gama dole ku mayar da azurfan da aka sa a cikin bakunan buhunanku. Mai yiwuwa an yi haka a kuskure ne.
13 Take also youre brother with you and aryse and goo agayne to the man.
Ku ɗauki ɗan’uwanku kuma ku koma wurin mutumin nan da nan.
14 And God almightie geue you mercie in the sighte of the man and send you youre other brother and also Be Iamin and I wilbe as a ma robbed of his childern.
Bari Allah Maɗaukaki yă nuna muku alheri a gaban mutumin saboda yă bar ɗan’uwanku da Benyamin su dawo tare da ku. Ni kuwa, in na yi rashi, na yi rashi.”
15 Thus toke they the present and twise so moch more money with them and Ben Iamin. And rose vp went downe to Egipte and presented them selfe to Ioseph.
Saboda haka mutanen suka ɗauki kyautar, da kuma kuɗin da ya ninka na farko. Suka kuma ɗauki Benyamin, suka gaggauta suka gangara zuwa Masar suka kuma gabatar da kansu ga Yusuf.
16 When Ioseph sawe Ben Iamin with them he sayde to the ruelar of his house: brynge these men home and sley and make redie: for they shall dyne with me at none.
Sa’ad da Yusuf ya ga Benyamin tare da su, sai ya ce wa mai hidimar gidansa, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.”
17 And the man dyd as Ioseph bad and brought them in to Iosephs house.
Mutumin ya yi kamar yadda Yusuf ya faɗa masa, ya kuwa ɗauki mutanen zuwa gidan Yusuf.
18 When they were brought to Iosephs house they were afrayde ad sayde: be cause of the money yt came in oure sackes mouthes at the first tyme are we brought to pyke a quarell with vs and to laye some thinge to oure charge: to brynge us in bondage and oure asses also.
Mutanen dai suka firgita sa’ad da aka ɗauke su zuwa gidansa. Suka yi tunani, “An kawo mu nan ne saboda azurfan da aka sa a cikin buhunanmu da farko. Yana so yă fāɗa mana, yă kuma sha ƙarfinmu, yă ƙwace mu kamar bayi, yă kuma kwashe jakunanmu.”
19 Therfore came they to the man that was the ruelar ouer Iosephs house and comened with him at the doore
Saboda haka suka je wurin mai yin wa Yusuf hidima, suka yi masa magana a bakin ƙofar gida.
20 and sayde: Sir we came hither at the first tyme to bye foode
Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun zo nan ƙaro na farko don mu saya abinci,
21 and as we came to an Inne and opened oure sackes: beholde euery mannes money was in his sacke with full weghte: But we haue broght it agene with us
amma a inda muka tsaya don mu kwana, da muka buɗe buhunanmu sai kowannenmu ya sami azurfansa daidai a bakin buhunsa. Saboda haka ga kuɗin a hannunmu, mun sāke komowa da su.
22 and other mony haue we brought also in oure handes to bye foode but we can not tell who put oure money in oure sackes.
Mun kuma kawo ƙarin azurfa tare da mu don mu saya abinci. Ba mu san wa ya sa azurfanmu a cikin buhunanmu ba.”
23 And he sayde: be of good chere feare not: Youre God and the God of youre fathers hath put you that treasure in youre sackes for I had youre money. And he brought Simeon out to them
Sai mai hidimar ya ce, “Ba kome, kada ku ji tsoro. Allahnku, Allahn mahaifinku ne ya ba ku dukiyar a cikin buhunanku; ni dai, na karɓi azurfanku.” Sa’an nan ya fitar musu da Simeyon.
24 ad led the into Iosephs house and gaue the water to washe their fete and gaue their asses prauender:
Mai yin hidimar ya ɗauki mutane zuwa gidan Yusuf ya ba su ruwa su wanke ƙafafunsu, ya kuma tanada wa jakunansu abinci.
25 And they made redie their present agaynst Ioseph came at none for they herde saye that they shulde dyne there.
Suka shirya kyautansu domin isowar Yusuf da rana, gama sun ji cewa zai ci abinci a nan.
26 When Ioseph came home they brought the present in to the house to him which they had in their handes ad fell flat on the grounde befor him.
Sa’ad da Yusuf ya zo gida, sai suka ba shi kyautai da suka kawo, suka rusuna a gabansa har ƙasa.
27 And he welcomed the curteously sainge: is youre father that old man which ye tolde me of in good health? and is he yet alyue?
Ya tambaye su, yaya suke, sa’an nan ya ce, “Yaya tsohon nan mahaifinku da kuka faɗa mini? Yana da rai har yanzu?”
28 they answered: thy servaunte oure father is in good health ad is yet alyue. And they bowed them selues and fell to the grounde.
Suka amsa, “Bawanka mahaifinmu yana da rai har yanzu da kuma ƙoshin lafiya.” Suka kuma rusuna suka yi mubaya’a.
29 And he lyfte vp his eyes and behelde his brother Ben Iamin his mothers sonne and sayde: is this youre yongest brother of whome ye sayde vnto me? And sayde: God be mercyfull vnto ye my sonne.
Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
30 And Ioseph made hast (for his hert dyd melt apon his brother) and soughte for to wepe and entred in to his chambre for to wepe there.
Saboda motsi mai zurfi da zuciyarsa ta yi da ganin ɗan’uwansa, sai Yusuf ya gaggauta ya fita, ya nemi wuri yă yi kuka. Ya shiga ɗakinsa ya yi kuka a can.
31 And he wasshed his face and came out and refrayned himselfe and bad sett bread on the table
Bayan ya wanke fuskarsa, sai ya fito ya daure, ya umarta, “A kawo abinci.”
32 And they prepared for him by himselfe and for them by them selues and for the Egiptians which ate with him by them selues because the Egyptians may not eate bread with the Hebrues for that is an abhomynacyon vnto the Egiptians.
Sai aka raba musu abinci, nasa shi kaɗai su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sa cin abinci tare da Ibraniyawa, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa.
33 And they satt before him: the eldest acordynge vnto his age and the yongest acordyng vnto his youth. And the men marveled amonge them selves.
Aka zaunar da’yan’uwan Yusuf a gabansa bisa ga shekarunsu, daga ɗan fari zuwa auta.’Yan’uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki.
34 And they broughte rewardes vnto them from before him: but Ben Iamins parte was fyue tymes so moch as any of theirs. And they ate and they dronke and were dronke wyth him.
Daga teburin da yake a gaban Yusuf aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Benyamin ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.