< Matthew 21 >

1 When they had almost reached Jerusalem, having come as far as Bethphage, on the Mount of Olives, Jesus sent on two disciples.
Da suka yi kusa da Urushalima suka kuma kai Betfaji da yake kan Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajirai biyu,
2 “Go to the village facing you,” he said, “and you will immediately find an ass tethered, with a foal by her side; untie her, and lead her here for me.
yana ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gabanku, nan take za ku ga wata jaka a daure tare da ɗanta kusa da ita, a can. Ku kunce su ku kawo mini.
3 And, if any one says anything to you, you are to say this — ‘The Master wants them’; and he will send them at once.”
In wani ya yi muku wata magana, ku ce masa Ubangiji yana bukatarsu, zai kuwa mai da su nan da nan.”
4 This happened in fulfilment of these words in the Prophet —
Wannan ya faru ne don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabin cewa,
5 ‘Say to the daughter of Zion — “Behold, thy King is coming to thee, Gentle, and riding on an ass, and on the foal of a beast of burden.”’
“Ku ce wa Diyar Sihiyona, ‘Duba, sarkinki yana zuwa gare ki, mai tawali’u yana a kan jaki, a kan aholaki, ɗan jaki.’”
6 So the disciples went and did as Jesus had directed them.
Almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
7 They led the ass and the foal back, and, when they had put their cloaks on them, he seated himself upon them.
Suka kawo jakar da ɗanta, suka shimfiɗa mayafansu a kansu, Yesu kuma ya zauna a kansu.
8 The immense crowd of people spread their cloaks in the road, while some cut branches off the trees, and spread them on the road.
Wani babban taron mutane suka shimfiɗa mayafansu a kan hanya, yayinda waɗansu suka sassari rassan itatuwa suka shisshimfiɗa a kan hanya.
9 The crowds that led the way, as well as those that followed behind, kept shouting: “God save the Son of David! Blessed is he who comes in the name of the Lord! God save him from on high!”
Taron mutanen da suke gabansa da kuma waɗanda suke binsa a baya suka yi ihu suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Hosanna a cikin sama!”
10 When he had entered Jerusalem, the whole city was stirred, and asked —
Sa’ad da Yesu ya shiga Urushalima, dukan birnin ya ruɗe, ana ta tambaya, “Wane ne wannan?”
11 “Who is this?”, to which the crowd replied — “This is the Prophet Jesus from Nazareth in Galilee.”
Taron mutane suka amsa, “Wannan shi ne Yesu, annabin nan daga Nazaret a Galili.”
12 Jesus went into the Temple Courts, and drove out all those who were buying and selling there. He overturned the tables of the money-changers, and the seats of the pigeon-dealers,
Yesu ya shiga filin haikali, ya kuma kori duk masu saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur masu canjin kuɗi da kuma kujerun masu sayar da tattabarai.
13 and said to them: “Scripture says ‘My House shall be called a house of prayer’; but you are making it ‘a den of robbers.’”
Ya ce musu, “A rubuce yake, ‘Za a ce da gidana, gidan addu’a,’amma kuna mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
14 While he was still in the Temple Courts, some blind and some lame people came up to him, and he cured them.
Makafi da guragu suka zo wurinsa a haikali, ya kuwa warkar da su.
15 But, when the Chief Priests and the Teachers of the Law saw the wonderful things that Jesus did, and the boys who were calling out in the Temple Courts “God save the Son of David!”, they were indignant,
Amma da manyan firistoci da malaman dokoki suka ga abubuwan banmamakin da ya yi, yara kuma suna ihu a filin haikali suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda,” sai fushi ya kama su.
16 and said to him: “Do you hear what these boys are saying?” “Yes,” answered Jesus; “but did you never read the words — ‘Out of the mouths of babes and sucklings thou hast called forth perfect praise’?”
Suka tambaye shi suka ce, “Kana jin abin da waɗannan suke faɗa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, ba ku taɓa karanta ba cewa, “‘Daga leɓunan yara da jarirai kai, Ubangiji, ka shirya wa kanka yabo’?”
17 Then he left them, and went out of the city to Bethany, and spent the night there.
Sai ya bar su, ya fita daga birnin ya tafi Betani, inda ya kwana.
18 The next morning, in returning to the city, Jesus became hungry;
Kashegari da sassafe, yayinda yake kan hanyarsa ta komawa cikin birni, sai ya ji yunwa.
19 and, noticing a solitary fig tree by the road-side, he went up to it, but found nothing on it but leaves. So he said to it: “Never again shall fruit be gathered off you.” And suddenly the fruit tree withered up. (aiōn g165)
Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn g165)
20 When the disciples saw this, they exclaimed in astonishment: “How suddenly the fig tree withered up!”
Sa’ad da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya itacen ɓauren ya yanƙwane nan da nan haka?”
21 “I tell you,” replied Jesus, “if you have faith, without ever a doubt, you will do what not only what has been done to the fig tree, but, even if you should say to this hill ‘Be lifted up and hurled into the sea!’ it would be done.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiya, ba kuwa da wata shakka ba, ba kawai za ku iya yin abin da aka yi wa itacen ɓauren nan ba, amma za ku ma iya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka jefa kanka cikin teku,’ sai yă faru.
22 And whatever you ask for in your prayers will, if you have faith, be granted you.”
In kun gaskata, za ku karɓi duk abin da kuka roƙa a cikin addu’a.”
23 After Jesus had come into the Temple Courts, the Chief Priests and the Councillors of the Nation came up to him as he was teaching, and said: “What authority have you to do these things? Who gave you this authority?”
Sai Yesu ya shiga filin haikali, yayinda yake koyarwa, sai manyan firistoci da dattawan mutane suka zo wurinsa suka yi tambaya, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Kuma wa ya ba ka wannan iko?”
24 “I, too,” said Jesus in reply, “will ask you one question; if you will give me an answer to it, then I, also, will tell you what authority I have to act as I do.
Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku tambaya guda. In kuka ba ni amsa, ni ma zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
25 It is about John’s baptism. What was its origin? divine or human?” But they began arguing among themselves: “If we say ‘divine,’ he will say to us ‘Why then did not you believe him?’
Baftismar Yohanna, daga ina ta fito? Daga sama ce, ko daga mutane?” Sai suka tattauna a junansu suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama,’ zai ce, ‘To, me ya sa ba mu gaskata shi ba?’
26 But if we say ‘human,’ we are afraid of the people, for every one regards John as a Prophet.”
In kuma muka ce, ‘Daga mutane,’ muna tsoron mutane, gama duk sun ɗauka Yohanna annabi ne.”
27 So the answer they gave Jesus was — “We do not know.” “Then I,” he said, “refuse to tell you what authority I have to do these things.
Saboda haka suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Sai ya ce, “Ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”
28 What do you think of this? There was a man who had two sons. He went to the elder and said ‘Go and work in the vineyard to-day my son.’
“Me kuka gani? An yi wani mutum wanda yake da’ya’ya biyu maza. Sai ya je wajen ɗan farin ya ce, ‘Ɗana, yau tafi gonar inabi ka yi aiki.’
29 ‘Yes, sir,’ he answered; but he did not go.
“Ya amsa ya ce, ‘Ba zan tafi ba,’ amma daga baya ya sāke tunani, ya tafi.
30 Then the father went to the second son, and said the same. ‘I will not,’ he answered; but afterwards he was sorry and went.
“Sai mahaifin ya tafi waje na biyun ya faɗa masa iri magana guda. Sai ya amsa ya ce, ‘Zan tafi, ranka yă daɗe,’ amma bai tafi ba.
31 Which of the two sons did as his father wished?” “The second,” they said. “I tell you,” added Jesus, “that tax-gatherers and prostitutes are going into the Kingdom of God before you.
“Wanne cikin yaran nan biyu ya yi abin da mahaifinsa yake so?” Suka amsa, “Na farin.” Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga mulkin Allah.
32 For when John came to you, walking in the path of righteousness, you did not believe him, but tax-gatherers and prostitutes did; and yet you, though you saw this, even then were not sorry, nor did you believe him.
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo wurinku don yă nuna muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba, amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata. Har ma bayan kun ga wannan, ba ku tuba kun gaskata shi ba.”
33 Listen to another parable. A man, who was an employer, once planted a vineyard, put a fence round it, dug a winepress in it, built a tower, and then let it out to tenants and went abroad.
“Ku saurari wani misali. An yi wani mai gona wanda ya yi gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa wurin matsin inabi a ciki, ya kuma gina hasumiyar gadi. Sa’an nan ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, ya kuma yi tafiya.
34 When the time for the vintage drew near, he sent his servants to the tenants, to receive his share of the produce.
Da lokacin girbi ya yi kusa, sai ya aiki bayinsa wajen’yan hayan, su karɓo masa’ya’yan inabi.
35 But the tenants seized his servants, beat one, killed another, and stoned a third.
“Amma’yan hayan suka kama bayinsa; suka dūke ɗaya, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi na ukun.
36 A second time the owner sent some servants, a larger number than before, and the tenants treated them in the same way.
Sai ya sāke aiken waɗansu bayi wurinsu, fiye da na dā yawa, amma’yan hayan suka yi musu kamar yadda suka yi wa na farin.
37 As a last resource he sent his son to them. ‘They will respect my son,’ he said.
A ƙarshe, sai ya aiki ɗansa a wurinsu. Ya ce, ‘Za su girmama ɗana.’
38 But the tenants, on seeing his son, said to each other ‘Here is the heir! Come, let us kill him, and get his inheritance.’
“Amma da’yan hayan suka hangi ɗan, sai suka ce wa juna, ‘Wannan shi ne magājin. Ku zo, mu kashe shi, mu ci gādonsa.’
39 So they seized him, and threw him outside the vineyard, and killed him.
Saboda haka suka kama shi, suka jefar da shi bayan katangar gonar inabin, suka kashe shi.
40 Now, when the owner of the vineyard comes, what will he do to those tenants?”
“To, idan mai gonar inabin ya zo, me zai yi da’yan hayan nan?”
41 “Miserable wretches!” they exclaimed, “he will put them to a miserable death, and he will let out the vineyard to other tenants, who will pay him his share of the produce at the proper times.”
Suka amsa suka ce, “Zai yi wa banzan mutanen nan mugun kisa, yă ba da hayar gonar inabin ga waɗansu’yan haya, waɗanda za su ba shi rabonsa na amfanin gona a lokacin girbi.”
42 Then Jesus added: “Have you never read in the Scriptures? — ‘The very stone which the builders despised — Has now itself become the corner-stone; This corner-stone has come from the Lord, and is marvellous in our eyes.’
Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta a cikin Nassi cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi shi ne ya zama dutsen kusurwar gini. Ubangiji ne ya aikata wannan, kuma abin mamaki ne a idanunmu’?
43 And that, I tell you, is why the Kingdom of God will be taken from you, and given to a nation that does produce the fruit of the Kingdom.
“Saboda haka, ina gaya muku cewa za a karɓe mulkin Allah daga gare ku, a ba wa mutanen da za su ba da amfani.
44 Yes, and he who falls on this stone will be dashed to pieces, while any one on whom it falls — it will scatter him as dust.”
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Amma duk wanda dutsen nan ya fāɗi a kansa, za a murƙushe shi.”
45 After listening to these parables, the Chief Priests and the Pharisees saw that it was about them that he was speaking;
Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan Yesu, sai suka gane cewa da su yake.
46 yet, although eager to arrest him, they were afraid of the crowds, who regarded him as a Prophet.
Suka nemi hanyar kama shi, amma suka ji tsoron taron, don mutane sun ɗauka shi annabi ne.

< Matthew 21 >