< Mark 3 >

1 On another occasion Jesus went in to a Synagogue, where there was a man whose hand was withered.
Sai kuma ya sake tafiya cikin Majami'a sai ga wani Mutum mai shanyayyen hannu.
2 And they watched Jesus closely, to see if he would cure the man on the Sabbath, so that they might have a charge to bring against him.
Wadansu mutane suna kallonsa sosai, su gani ko zai warkar da shi a ranar Asabar. don su zarge shi.
3 “Stand out in the middle,” Jesus said to the man with the withered hand;
Yesu ya ce wa mai shanyayyen hanun “Ka tashi ka tsaya a tsakiyar kowa.”
4 and to the people he said: “Is it allowable to do good on the Sabbath — or harm? to save a life, or destroy it?”
Sai ya ce wa mutane, “Ya dace a yi abu mai kyau aranar Asabar ko a yi mugunta; a ceci rai, ko a yi kisa? “Amma suka yi shiru.
5 As they remained silent, Jesus looked round at them in anger, grieving at the hardness of their hearts, and said to the man: “Stretch out your hand.” The man stretched it out; and his hand had become sound.
Sai ya dube su cikin fushi, yana bakin ciki da taurin zuciyar su, ya ce wa mutumin ka mikar da hanunka, sai ya mikar da hanunsa Yesu kuwa ya warkar da shi.
6 Immediately on leaving the Synagogue, the Pharisees and the Herodians united in laying a plot against Jesus, to put him to death.
Sai Farisiyawa suka fita da sauri zuwa wurin mutanen Hirudus suka shirya yadda za su kashe shi.
7 Then Jesus went away with his disciples to the Sea, followed by a great number of people from Galilee.
Sai Yesu da almajiransa, suka tafi bakin teku. sai mutane dayawa suka bi shi, daga Galili da Yahudiya
8 And a great number, hearing of all that he was doing, came to him from Judea, from Jerusalem, from Edom, from beyond the Jordan, and from the country round Tyre and Sidon.
Daga Urushalima da Edom gaba da Urdun da kewayan Taya da Sidon, da baban taro, ya ji abinda yake yi. suka zo wurinsa.
9 So Jesus told his disciples to keep a small boat close by, for fear the crowd should crush him.
Ya tambayi almajiransa su shirya masa karamin jirgin ruwa domin yawan mutane, domin kada su murkushe shi.
10 For he had cured many of them, and so people kept crowding upon him, that all who were afflicted might touch him.
Ya warkar da mutane da yawa, yadda duk wadanda suke da cuttutuka suna kokari su taba shi.
11 The foul spirits, too, whenever they caught sight of him, flung themselves down before him, and screamed out: “You are the Son of God”!
Duk sa'adda kazaman ruhohin suka ganshi, sai su durkusa a gabansa su yi ihu da karfi su ce, kai Dan Allah ne.”
12 But he repeatedly warned them not to make him known.
Ya umarce su da karfi kada su sa a san shi.
13 And Jesus made his way up the hill, and called those whom he wished; and they went to him.
Ya hau saman dutsen, ya kira wadanda yake bukar su, su zo wurinsa.
14 And he appointed twelve — whom he also named ‘Apostles’ — that they might be with him, and that he might send them out as his Messengers, to preach,
Ya zabi guda goma sha biyu (ya kira su manzanni). Wadanda zasu kasance tare da shi, ya kuma aike su, su yi wa, azi,
15 and with power to drive out demons.
Ya kuma basu Ikon fitar da aljanu.
16 So he appointed the Twelve — Peter (which was the name that Jesus gave to Simon),
Ya zabi guda goma sha biyu wato Saminu kuma yaba shi suna Bitrus.
17 James, the son of Zebediah, and his brother John (to whom he gave the name of Boanerges, which means the Thunderers),
Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan-uwan Yakubu wanda ya basu sunan Buwanarjis watau 'ya'yan tsawa,
18 Andrew, Philip, Bartholomew, Matthew, Thomas, James the son of Alphaeus, Thaddaeus, Simon the Zealot,
da Andarawus da Filibus da Bartalamawus da Matta da Toma da Yakubu dan Halfa, da Taddawus da Saminu Ba-kananiye,
19 and Judas Iscariot, the man that betrayed him.
da Yahuza Iskariyoti wanda zai bashe shi.
20 Jesus went into a house; and again a crowd collected, so that they were not able even to eat their food.
Sa'adda ya shiga gida, Taron kuwa ya sake haduwa, har ya hana su cin abinci,
21 When his relations heard of it, they went to take charge of him, for they said that he was out of his mind.
Da iyalansa suka ji haka, sai suka fito sun kamo shi, saboda sun ce, “Ai, baya cikin hankalinsa “
22 And the Teachers of the Law, who had come down from Jerusalem, said: “He has Baal-zebub in him, and he drives the demons out by the help of Baal-zebub, their chief.”
Marubutan da suka zo daga Urushalima suka ce “Ai Ba'alzabuba ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu.”
23 So Jesus called them to him, and answered them in parables: “How can Satan drive out Satan?
Yesu ya kirawo su wurinsa ya ce da su cikin misalai, “Yaya shaidan zai iya fitar da shaidan?
24 When a kingdom is divided against itself, it cannot last;
idan mulki ya rabu gida biyu ba zai tsayawa ba.
25 and when a household is divided against itself, it will not be able to last.
Haka in gida ya rabu kashi biyu, gaba da kansa bai zai tsaya ba.
26 So, if Satan is in revolt against himself and is divided, he cannot last — his end has come!
Shaidan kuma in ya tayar wa kansa ya rabu, ba zai iya tsayawa ba, gama karshen sa ya zo kenan.
27 “No man who has got into a strong man’s house can carry off his goods, without first securing him; and not till then will he plunder his house.
Amma ba mai iya shiga gidan kakkarfan mutum ya kwace kayansa, ba tare da ya fara daure kakkarfan mutumin ba, sa'an nan kuma ya kwashe kayan gidansa.
28 I tell you that men will be forgiven everything — their sins, and all the slanders that they utter;
Hakika, ina gaya maku, dukan zunuban da mutane suka yi za a gafarta masu, da kowane irin sabon da suka furta,
29 but whoever slanders the Holy Spirit remains unforgiven to the end; he has to answer for an enduring sin.” (aiōn g165, aiōnios g166)
amma fa duk wanda yayi sabon Ruhun Mai Tsarki baza a gafarta masa ba ko kadan, ya zama mai zunubi har abada.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 This was said in reply to the charge that he had a foul spirit in him.
“Yesu ya fadi wadannan abubuwa domin suna cewa yana da ba kazamin ruhu,”
31 And his mother and his brothers came, and stood outside, and sent to ask him to come to them.
Sa'an nan uwatasa, da “Yan'uwansa suka zo suna tsaye a waje. sai suka aika masa, suna kuma umurtar sa ya zo.
32 There was a crowd sitting round Jesus, and some of them said to him: “Look, your mother and your brothers are outside, asking for you.”
Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka yi magana da shi da cewa, ga uwarka da yan-uwanka suna nan a waje, suna nemanka.”
33 “Who is my mother? and my brothers?” was his reply.
Ya amsa masu, “Dacewa su wanene uwa-ta da “yan'uwa na? “
34 Then he looked around on the people sitting in a circle round him, and said: “Here are my mother and my brothers!
Sai ya waiwayi wadanda suke zaune kewaye da shi, yace, “Ga uwa-ta da yan-uwana anan!
35 Whoever does the will of God is my brother and sister and mother.”
Gama duk wanda ke yin abin da Allah yake so, shine dan'uwana da yar, uwata, da kuma uwa-ta.”

< Mark 3 >