< Luke 7 >

1 When Jesus had brought to a conclusion all that he had then had to say to the people, he entered Capernaum.
Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
2 A Captain in the Roman army had a slave whom he valued, and who was seriously ill — almost at the point of death.
A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
3 And, hearing about Jesus, he sent some Jewish Councillors to him, with the request that he would come and save his slave’s life.
Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
4 When they found Jesus, they earnestly implored him to do so. “He is a man who deserves that you should show him this favour,” they said,
Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
5 “For he is devoted to our nation, and himself built our Synagogue for us.”
gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
6 So Jesus went with them. But, when he was no great distance from the house, the Captain sent some friends with the message — “Do not trouble yourself, Sir; for I am unworthy to receive you under my roof.
Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
7 That was why I did not even venture to come to you myself; but speak, and let my manservant be cured.
Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
8 For I myself am a man under the orders of others, with soldiers under me; and if I say to one of them ‘Go,’ he goes, and to another ‘Come,’ he comes, and to my slave ‘Do this,’ he does it.”
Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
9 Jesus was surprised to hear these words from him; and, turning to the crowd which was following him, he said: “I tell you, nowhere in Israel have I met with such faith as this!”
Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
10 And, when the messengers returned to the house, they found the slave recovered.
Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
11 Shortly after, Jesus went to a town called Nain, his disciples and a great crowd going with him.
Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
12 Just as he approached the gate of the town, there was a dead man being carried out for burial — an only son, and his mother was a widow. A large number of the people of the town were with her.
Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
13 When he saw her, the Master was moved with compassion for her, and he said to her: “Do not weep.”
Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
14 Then he went up and touched the bier, and the bearers stopped; and Jesus said: “Young man, I am speaking to you — Rise!”
Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
15 The dead man sat up and began to talk, and Jesus restored him to his mother.
Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
16 Every one was awe-struck and began praising God. “A great Prophet has arisen among us,” they said; “and God has visited his people.”
Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
17 And this story about Jesus spread all through Judea, and in the neighbouring countries as well.
Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
18 All these events were reported to John by his disciples.
Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
19 So he summoned two of them, and sent them to the Master to ask — “Are you ‘The Coming One,’ or are we to look for some one else?”
ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
20 When these men found Jesus, they said: “John the Baptist has sent us to you to ask — ‘Are you ‘The Coming One,’ or are we to look for somebody else?’”
Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
21 At that very time Jesus had cured many people of diseases, afflictions, and wicked spirits, and had given many blind people their sight.
A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
22 So his answer to the question was: “Go and report to John what you have witnessed and heard — the blind recover their sight, the lame walk, the lepers are made clean, and the deaf hear, the dead are raised to life, the Good News is told to the poor.
Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
23 And blessed is the man who finds no hindrance in me.”
Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
24 When John’s messengers had left, Jesus, speaking to the crowds, began to say with reference to John:
Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
25 “What did you go out into the Wilderness to look at? A reed waving in the wind? If not, what did you go out to see? A man dressed in rich clothing? Why, those who are accustomed to fine clothes and luxury live in royal palaces.
In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
26 What then did you go to see? A Prophet? Yes, I tell you, and far more than a Prophet.
Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
27 This is the very man of whom Scripture says — ‘Behold, I am sending my Messenger before thy face, And he shall prepare thy way before thee.’
Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
28 There is, I tell you, no one born of a woman who is greater than John; and yet the lowliest in the Kingdom of God is greater than he.”
Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
29 (All the people, when they heard this, and even the tax-gatherers, having accepted John’s baptism, acknowledged the justice of God.
(Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
30 But the Pharisees and the Students of the Law, having rejected John’s baptism, frustrated God’s purpose in regard to them.)
Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
31 “To what then,” Jesus continued, “shall I compare the people of the present generation? What are they like?
Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
32 They are like some little children who are sitting in the market-place and calling out to one another — ‘We have played the flute for you, but you have not danced; We have wailed, but you have not wept!’
Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
33 For now that John the Baptist has come, not eating bread or drinking wine, you are saying ‘He has a demon in him’;
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
34 and now that the Son of Man has come, eating and drinking, you are saying ‘Here is a glutton and a wine-drinker, a friend of tax-gatherers and outcasts.’
Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
35 And yet Wisdom is vindicated by all her children.”
Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
36 One of the Pharisees asked Jesus to dine with him, so Jesus went to his house and took his place at table.
To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
37 Just then a woman, who was an outcast in the town, having ascertained that Jesus was at table in the Pharisee’s house, brought an alabaster jar of perfume,
Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
38 and placed herself behind Jesus, near his feet, weeping. Then she began to make his feet wet with her tears, and she dried them with the hair of her head, repeatedly kissing his feet and anointing them with the perfume.
ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
39 When the Pharisee who had invited Jesus saw this, he said to himself: “Had this man been ‘The Prophet,’ he would have known who, and what sort of woman, this is who is touching him, and that she is an outcast.”
Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
40 But, addressing him, Jesus said: “Simon, I have something to say to you.” “Pray do so, Teacher,” Simon answered; and Jesus began:
Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
41 “There were two people who were in debt to a money-lender; one owed fifty pounds, and the other five.
Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
42 As they were unable to pay, he forgave them both. Which of them, do you think, will love him the more?”
Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
43 “I suppose,” answered Simon, “it will be the man to whom he forgave the greater debt.” “You are right,” said Jesus,
Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
44 and then, turning to the woman, he said to Simon: “Do you see this woman? I came into your house — you gave me no water for my feet, but she has made my feet wet with her tears and dried them with her hair.
Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
45 You did not give me one kiss, but she, from the moment I came in, has not ceased to kiss my feet.
Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
46 You did not anoint even my head with oil, but she has anointed my feet with perfume.
Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
47 And for this, I tell you, her sins, many as they are, have been pardoned, because she has loved greatly; but one who has little pardoned him, loves but little.”
“Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
48 Then he said to the woman: “Your sins have been pardoned.”
Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
49 On this, those at table began to say to one another: “Who is this man who even pardons sins?”
Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
50 But Jesus said to the woman: “Your faith has delivered you; go, and peace be with you.”
Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”

< Luke 7 >