< John 20 >
1 On the first day of the week, early in the morning, while it was still dark, Mary of Magdala went to the tomb, and saw that the stone had been removed.
To da sassafe ranar farko ta mako, da sauran duhu, Maryamu Magadaliya ta zo kabarin, ta tarar an kawar da dutsen daga kabarin.
2 So she came running to Simon Peter, and to that other disciple who was Jesus’ friend, and said to them: “They have taken away the Master out of the tomb, and we do not know where they have laid him!”
Sai ta ruga da gudu zuwa wurin Saminu Bitrus tare da almajirin nan da Yesu ke kauna, tace masu, “Sun dauke Ubangiji daga kabarin, bamu kuwa san inda aka sa shi ba.”
3 Upon this, Peter started off with that other disciple, and they went to the tomb.
Sai Bitrus tare da almajirin nan suka fita, kuma suka tafi kabarin,
4 The two began running together; but the other disciple ran faster than Peter, and reached the tomb first.
dukansu suka ruga da gudu tare, amma daya almajirin ya riga Bitrus isowa kabarin,
5 Stooping down, he saw the linen wrappings lying there, but did not go in.
Sai ya sunkuya ya leka ciki, ya ga likkafanin lillin a wurin, amma fa bai shiga ciki ba.
6 Presently Simon Peter came following behind him, and went into the tomb; and he looked at the linen wrappings lying there,
Sai Saminu Bitrus ya iso daga bayansa sai ya shiga kabarin, ya tarar da likkafanin lillin a ajiye.
7 and the cloth which had been upon Jesus’ head, not lying with the wrappings, but rolled up on one side, separately.
sai fallen kuma da yake kansa. Ba'a ajiye tare da likkafanin ba amma aka linkeshi aka ajiye shi daban.
8 Then the other disciple, who had reached the tomb first, went inside too, and he saw for himself and was convinced.
Sai almajirin nan da ya riga isa kabarin shi ma ya shiga ya gani, sai ya ba da gaskiya.
9 For they did not then understand the passage of Scripture which says that Jesus must rise again from the dead.
Har ya zuwa wannan lokacin basu san nassin daya ce zai tashi daga matattu ba.
10 The disciples then returned to their companions.
Sai almajiran suka sake komawa gida kuma.
11 Meanwhile Mary was standing close outside the tomb, weeping. Still weeping, she leant forward into the tomb,
Amma Maryamu tana tsaye a bakin kabarin tana kuka. Yayin da take kuka, sai ta sunkuya ta leka cikin kabarin.
12 and perceived two angels clothed in white sitting there, where the body of Jesus had been lying, one where the head and the other where the feet had been.
Sai ta ga mala'iku guda biyu cikin fararen kaya zaune, daya ta wurin kai daya kuma ta wurin kafafu inda aka kwantar da Yesu.
13 “Why are you weeping?” asked the angels. “They have taken my Master away,” she answered, “and I do not know where they have laid him.”
Sukace mata, “Uwargida don me kike kuka? Sai tace masu, “Domin sun dauke Ubangijina, ban kuwa san inda suka ajiye shi ba.
14 After saying this, she turned round, and looked at Jesus standing there, but she did not know that it was Jesus.
Bayan ta fadi haka, ta juya sai ta ga Yesu tsaye a wurin. Amma bata san cewa Yesu bane,
15 “Why are you weeping? Whom are you seeking?” he asked. Supposing him to be the gardener, Mary answered: “If it was you, Sir, who carried him away, tell me where you have laid him, and I will take him away myself.”
Yesu yace mata, “Uwargida, me yasa kike kuka? Wa kuma kike nema? Domin tana zaton shine mai kula da lambun, sai tace masa, “Maigida in kaine ka dauke shi, gaya mani inda ka sa shi, ni kuwa in dauke shi.”
16 “Mary!” said Jesus. She turned round, and exclaimed in Hebrew: “Rabboni!” (or, as we should say, ‘Teacher’).
Yesu yace mata, “Maryamu”. Sai ta juya, tace masa da Armaniyanci “Rabboni!” wato mallam.
17 “Do not hold me,” Jesus said; “for I have not yet ascended to the Father. But go to my Brothers, and tell them that I am ascending to him who is my Father and their Father, my God and their God.”
Yesu yace mata, kada ki taba ni, domin har yanzu ban hau wurin Uba ba tukuna, amma kije wurin 'yan'uwana kice masu, zan je wurin Ubana da Ubanku, Allahna da kuma Allahnku”.
18 Mary of Magdala went and told the disciples that she had seen the Master, and that he had said this to her.
Maryamu Magadaliya ta je tace wa almajiran, “Na ga Ubangiji” Ta kuma ce ya fada mata wadannan abubuwa.
19 In the evening of the same day — the first day of the week — after the doors of the room, in which the disciples were, had been shut for fear of the Jews, Jesus came and stood among them and said: “Peace be with you”;
Da yamma a wannan rana, a rana ta farko ta mako, almajiran suna kulle a daki saboda tsoron Yahudawa, Yesu yazo ya tsaya a tsakaninsu, yace “Salama Agareku”.
20 after which he showed them his hands and his side. The disciples were filled with joy when they saw the Master.
Bayan ya fadi haka, sai ya nuna masu hannuwansa da kuibinsa. Da almajiran suka ga Ubangiji, sai suka yi farin ciki.
21 Again Jesus said to them: “Peace be with you. As the Father has sent me as his Messenger, so I am sending you.”
Yesu ya sake ce masu, “salama agareku. “Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka Ni ma na aike ku”.
22 After saying this, he breathed on them, and said: “Receive the Holy Spirit;
Da Yesu ya fadi haka, sai ya hura masu lumfashinsa, yace masu, “Ku karbi Ruhu Mai Tsarki.
23 if you remit any one’s sins, they have been remitted; and, if you retain them, they have been retained.”
Duk wanda kuka gafarta wa zunubai, an gafarta masa; kowa kuka rike zunubansa, an rikesu.”
24 But Thomas, one of the Twelve, called ‘The Twin,’ was not with them when Jesus came;
Toma, daya daga cikin sha biyun, wanda ake kira Dan Tagwai, baya tare dasu lokacin da Yesu ya bayyana.
25 so the rest of the disciples said to him: “We have seen the Master!” “Unless I see the marks of the nails in his hands,” he exclaimed, “and put my finger into the marks, and put my hand into his side, I will not believe it.”
Sauran almajiran sukace masa “Mun ga Ubangiji”. Sai yace masu, “In ban ga gurbin kusoshi a hannuwansa ba, in sa yatsana a gurbin kusoshin ba, in kuma sa hannuna cikin kuibinsa ba, ba zan bada gaskiya ba.
26 A week later the disciples were again in the house, and Thomas with them. After the doors had been shut, Jesus came and stood among them, and said: “Peace be with you.”
Bayan kwana takwas har wa yau almajiran na cikin gida, Toma ma na tare dasu, kofofin suna kulle, sai ga Yesu a tsakaninsu yace, “Salama agareku”.
27 Then he said to Thomas: “Place your finger here, and look at my hands; and place your hand here, and put it into my side; and do not refuse to believe, but believe.”
Sa'an nan yace wa Toma, “Iso nan da yatsanka, dubi hannuwana. Miko hannunka kuma kasa a kuibina, kada ka zama marar bada gaskiya, sai dai, mai bada gaskiya”.
28 And Thomas exclaimed: “My Master, and my God!”
Toma ya amsa yace “Ya Ubangijina da Allahna!”
29 “Is it because you have seen me that you have believed?” said Jesus. “Blessed are they who have not seen, and yet have believed!”
Yesu yace masa, “Wato saboda ka gan ni, ka bada gaskiya? Albarka ta tabbata ga wadanda basu gani ba, amma kuwa sun bada gaskiya.
30 There were many other signs of his mission that Jesus gave in presence of the disciples, which are not recorded in this book;
Yesu yayi wadansu alamu da yawa dabam dabam a gaban almajiransa, wadanda ba'a rubuta a littafin nan ba.
31 but these have been recorded that you may believe that Jesus is the Christ, the Son of God — and that, through your belief in his Name, you may have Life.
Amma an rubuta wadannan ne, domin ku bada gaskiya Yesu shine Almasihu, Dan Allah, ta wurin gaskatawa kuma ku sami rai cikin sunansa.