< John 2 >

1 Two days after this there was a wedding at Cana in Galilee, and Jesus’ mother was there.
A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can,
2 Jesus himself, too, with his disciples, was invited to the wedding.
aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren.
3 And, when the wine ran short, his mother said to him: “They have no wine left.”
Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
4 “What do you want with me?” answered Jesus. “My time has not come yet.”
Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”
5 His mother said to the servants: “Do whatever he tells you.”
Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
6 There were standing there six stone water-jars, in accordance with the Jewish rule of ‘purification,’ each holding twenty or thirty gallons.
Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.
7 Jesus said to the servants: “Fill the water-jars with water.”
Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.
8 And, when they had filled them to the brim, he added: “Now take some out, and carry it to the Master of the Feast.” The servants did so.
Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.” Suka yi haka.
9 And, when the Master of the Feast had tasted the water which had now become wine, not knowing where it had come from — although the servants who had taken out the water knew —
Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya
10 He called the bridegroom and said to him: “Every one puts good wine on the table first, and inferior wine afterwards, when his guests have drunk freely; but you have kept back the good wine till now!”
ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”
11 This, the first sign of his mission, Jesus gave at Cana in Galilee, and by it revealed his glory; and his disciples believed in him.
Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.
12 After this, Jesus went down to Capernaum — he, his mother, his brothers, and his disciples; but they stayed there only a few days.
Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna’yan kwanaki.
13 Then, as the Jewish Passover was near, Jesus went up to Jerusalem.
Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima.
14 In the Temple Courts he found people who were selling bullocks, sheep, and pigeons, and the money-changers at their counters.
A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi.
15 So he made a whip of cords, and drove them all out of the Temple Courts, and the sheep and bullocks as well; he scattered the money of the money-changers, and overturned their tables,
Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu.
16 and said to the pigeon-dealers: “Take these things away. Do not turn my Father’s House into a market-house.”
Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!”
17 His disciples remembered that Scripture said — ‘Zeal for thy House will consume me.’
Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”
18 Upon this the Jews asked Jesus: “What sign are you going to show us, since you act in this way?”
Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”
19 “Destroy this temple,” was his answer, “and I will raise it in three days.”
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”
20 “This Temple,” replied the Jews, “has been forty-six years in building, and are you going to ‘raise it in three days’?”
Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?”
21 But Jesus was speaking of his body as a temple.
Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne.
22 Afterwards, when he had risen from the dead, his disciples remembered that he had said this; and they believed the passage of Scripture, and the words which Jesus had spoken.
Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.
23 While Jesus was in Jerusalem, during the Passover Festival, many came to trust in him, when they saw the signs of his mission that he was giving.
To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
24 But Jesus did not trust himself to them, since he could read every heart,
Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
25 and because he did not need that others should tell him what men were; for he could of himself read what was in men.
Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.

< John 2 >