< John 12 >
1 Six days before the Passover Jesus came to Bethany, where Lazarus, whom he had raised from the dead, was living.
Kwana shida kafin Bikin Ƙetarewa, sai Yesu ya iso Betani, inda Lazarus yake, wanda Yesu ya tā da daga matattu.
2 There a supper was given in honour at which Martha waited, while Lazarus was one of those present at the table.
A nan aka shirya abincin yamma don girmama Yesu. Marta ta ce yi hidima, Lazarus kuma yana ɗaya cikin waɗanda suke ci tare shi.
3 So Mary took a pound of choice spikenard perfume of great value, and anointed the feet of Jesus with it, and then wiped them with her hair. The whole house was filled with the scent of the perfume.
Sai Maryamu ta ɗauki wajen awo guda na nardi zalla, turare mai tsada; ta zuba a ƙafafun Yesu ta kuma goge ƙafafunsa da gashinta. Gidan duk ya cika da ƙanshin turaren.
4 One of the disciples, Judas Iscariot, who was about to betray Jesus, asked:
Amma ɗaya daga cikin almajiransa, Yahuda Iskariyot, wanda daga baya zai bashe shi, bai amince ba ya ce,
5 “Why was not this perfume sold for thirty pounds, and the money given to poor people?”
“Don me ba a sayar da turaren nan aka kuma ba da kuɗin ga matalauta ba? Ai, kuɗin ya kai albashin shekara guda.”
6 He said this, not because he cared for the poor, but because he was a thief, and, being in charge of the purse, used to take what was put in it.
Ya yi wannan magana ba don ya kula da matalauta ba ne, sai dai don shi ɓarawo ne. Da yake shi ne mai ajiya jakar kuɗin, yakan taimaki kansa da abin da aka sa a ciki.
7 “Let her alone,” said Jesus, “that she may keep it till the day when my body is being prepared for burial.
Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta, an nufa ta ajiye wannan turaren don ranar jana’izata.
8 The poor you always have with you, but you will not always have me.”
Kullum za ku kasance da matalauta, amma ba kullum za ku kasance tare da ni ba.”
9 Now great numbers of the Jews found out that Jesus was at Bethany; and they came there, not solely on his account, but also to see Lazarus, whom he had raised from the dead.
Ana cikin haka sai babban taron Yahudawa suka sami labari Yesu yana can suka kuwa zo, ba kawai don shi ba amma don su kuma ga Lazarus, wanda ya tā da daga matattu.
10 The Chief Priests, however, plotted to put Lazarus, as well as Jesus, to death,
Saboda haka manyan firistoci suka ƙulla su kashe Lazarus shi ma,
11 because it was owing to him that many of the Jews had left them, and were becoming believers in Jesus.
gama dalilinsa Yahudawa da yawa suna komawa ga Yesu suna kuma ba da gaskiya gare shi.
12 On the following day great numbers of people who had come to the Festival, hearing that Jesus was on his way to Jerusalem, took palm-branches,
Kashegari babban taron da suka zo Bikin suka sami labari cewa Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima.
13 and went out to meet him, shouting as they went: “‘God save Him! Blessed is He who Comes in the name of the Lord’ — The King of Israel!”
Sai suka ɗaɗɗauko rassan dabino suka fiffita taryensa, suna ɗaga murya suna cewa, “Hosanna!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Mai albarka ne Sarkin Isra’ila!”
14 Having found a young ass, Jesus seated himself on it, in accordance with the passage of Scripture —
Yesu ya sami ɗan jaki, ya hau, kamar yadda yake a rubuce cewa,
15 ‘Fear not, Daughter of Zion; Behold, thy King is coming to thee, Sitting on the foal of an ass.’
“Kada ki ji tsoro, ya Diyar Sihiyona; duba, ga sarkinki yana zuwa, zaune a kan aholaki jaki.”
16 His disciples did not understand all this at first; but, when Jesus had been exalted, then they remembered that these things had been said of him in Scripture, and that they had done these things for him.
Da fari almajiransa ba su gane dukan wannan ba. Sai bayan da aka ɗaukaka Yesu, sa’an nan suka gane cewa an rubuta waɗannan abubuwa game da shi ne, har ma suka yi masa waɗannan abubuwa.
17 Meanwhile the people who were with him, when he called Lazarus out of the tomb and raised him from the dead, were telling what they had seen.
Taron da suke tare da shi a sa’ad da ya kira Lazarus daga kabari ya kuma tā da shi daga matattu suka yi ta baza labarin.
18 This, indeed, was why the crowd met him — because people had heard that he had given this sign of his mission.
Mutane da yawa kuwa suka fita taryensa, saboda sun ji labarin abin banmamakin da ya yi.
19 So the Pharisees said to one another: “You see that you are gaining nothing! Why, all the world has run after him!”
Saboda haka Farisiyawa suka ce wa juna, “Duba, wannan ba ya kai mu ko’ina. Ga shi, duk duniya tana bin sa!”
20 Among those who were going up to worship at the Festival were some Greeks,
To, akwai waɗansu Hellenawa a cikin waɗanda suka haura don su yi sujada a Bikin.
21 who went to Philip of Bethsaida in Galilee, and said: “Sir, we wish to see Jesus.”
Suka zo wurin Filibus, wanda yake daga Betsaida ta Galili, da roƙo. Suka ce, “Ranka yă daɗe, muna so mu ga Yesu.”
22 Philip went and told Andrew, and then together they went and told Jesus.
Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawus, Andarawus da kuma Filibus suka gaya wa Yesu.
23 This was his reply — “The time has come for the Son of Man to be exalted.
Yesu ya amsa ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum.
24 In truth I tell you, unless a grain of wheat falls into the ground and dies, it remains solitary; but, if it dies, it becomes fruitful.
Gaskiya nake gaya muku, sai ƙwayar alkama ta fāɗi ƙasa ta mutu, in ba haka ba za tă kasance ƙwaya ɗaya tak. Amma in ta mutu, za tă ba da’ya’ya da yawa.
25 He who loves his life loses it; while he who hates his life in the present world shall preserve it for Immortal Life. (aiōnios )
Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami. (aiōnios )
26 If a man is ready to serve me, let him follow me; and where I am, there my servant shall be also. If a man is ready to serve me, my Father will honour him.
Duk wanda zai bauta mini dole yă bi ni, inda kuma nake, a can bawana zai kasance. Ubana zai girmama wanda yake bauta mini.
27 Now I am distressed at heart and what can I say? Father, bring me safe through this hour — yet it was for this very reason that I came to this hour —
“Yanzu kuwa na damu, amma me zan ce? ‘Uba, ka cece ni daga wannan sa’a’? A’a, ai, saboda wannan dalili ne musamman na zo.
28 Father, honour thine own name.” At this there came a voice from Heaven, which said: “I have already honoured it, and I will honour it again.”
Uba, ka ɗaukaka sunanka!” Sai wata murya ta fito daga sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi.”
29 The crowd of bystanders, who heard the sound, said that it was thundering. Others said: “An angel has been speaking to him.”
Taron da suke a wurin suka ji, suka ce an yi tsawa; waɗansu kuwa suka ce mala’ika ne ya yi masa magana.
30 “It was not for my sake that the voice came,” said Jesus, “but for yours.
Yesu ya ce, “An yi wannan muryar saboda amfaninku ne, ba don nawa ba.
31 Now this world is on its trial. Now the Spirit that is ruling this world shall be driven out;
Yanzu ne za a yi wa duniyan nan shari’a, yanzu ne za a tumɓuke mai mulkin duniyan nan.
32 and I, when I am lifted up from the earth, shall draw all men to myself.”
Amma ni, sa’ad da aka ɗaga ni daga ƙasa, zan ja dukan mutane gare ni.”
33 By these words he indicated what death he was destined to die.
Ya faɗa haka ne don yă nuna irin mutuwar da zai yi.
34 “We,” replied the people, “have learned from the Law that the ‘Christ is to remain for ever’; how is it, then, that you say that the Son of Man must be ‘lifted up’ Who is this ‘Son of Man’?” (aiōn )
Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?” (aiōn )
35 “Only a little while longer,” answered Jesus, “will you have the Light among you. Travel on while you have the Light, so that darkness may not overtake you; he who travels in the darkness does not know where he is going.
Sai Yesu ya ce musu, “Haske zai kasance da ku na ɗan lokaci. Ku yi tafiya yayinda hasken yana nan tare da ku, kada duhu yă cim muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda za shi ba.
36 While you still have the Light, believe in the Light, that you may be ‘Sons of Light.’” After he had said this, Jesus went away, and hid himself from them.
Ku dogara ga hasken yayinda kuke da shi, don ku zama’ya’yan haske.” Da Yesu ya gama magana, sai ya tafi ya ɓuya daga gare su.
37 But, though Jesus had given so many signs of his mission before their eyes, they still did not believe in him,
Ko bayan Yesu ya yi dukan waɗannan abubuwan banmamaki a gabansu, duk da haka ba su gaskata da shi ba.
38 in fulfilment of the words of the Prophet Isaiah, where he says — ‘Lord, who has believed our teaching? And to whom has the might of the Lord been revealed?’
Wannan ya faru ne, don a cika maganar annabi Ishaya cewa, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu, ga wa kuma aka bayyana hannun ikon Ubangiji?”
39 The reason why they were unable to believe is given by Isaiah elsewhere, in these words —
Saboda haka ba su iya gaskatawa ba, domin, kamar yadda Ishaya ya faɗa a wani wuri cewa,
40 ‘He has blinded their eyes, and blunted their mind, so that they should not see with their eyes, and perceive with their mind, and turn — And I should heal them.’
“Ya makantar da idanunsu ya kuma taurare zukatansu, don kada su gani da idanunsu, ko su fahimta a zukatansu, ko kuwa su juyo, har in warkar da su.”
41 Isaiah said this, because he saw Christ’s glory; and it was of him that he spoke.
Ishaya ya faɗi haka ne, saboda ya hangi ɗaukakar Yesu, ya kuwa yi magana a kansa.
42 Yet for all this, even among the leading men there were many who came to believe in Jesus; but, on account of the Pharisees, they did not acknowledge it, for fear that they should be expelled from their Synagogues;
Duk da haka, da yawa har daga cikin shugabanni ma suka gaskata da shi. Amma saboda Farisiyawa ba su furta bangaskiyarsu ba, don tsoron kada a kore su daga majami’a;
43 for they valued honour from men more than honour from God.
gama sun fi son yabon mutane, fiye da yabon Allah.
44 But Jesus had proclaimed: “He who believes in me believes, not in me, but in him who sent me;
Sa’an nan Yesu ya ɗaga murya ya ce, “Duk wanda ya gaskata da ni, ba ni yake gaskatawa ba, amma ga wanda ya aiko ni ne.
45 and he who sees me sees him who sent me.
Duk mai dubana, yana duban wanda ya aiko ni ne.
46 I have come as a Light into the world, that no one who believes in me should remain in the darkness.
Na zo cikin duniya a kan ni haske ne, don duk wanda ya gaskata da ni, kada yă zauna a cikin duhu.
47 When any one hears my teaching and pays no heed to it, I am not his judge; for I came not to judge the world, but to save the world.
“Duk mai jin kalmomina bai kuwa kiyaye su ba, ba ni ba ne nake shari’anta shi. Gama ban zo domin in yi wa duniya shari’a ba, sai dai domin in cece ta.
48 He who rejects me, and disregards my teaching, has a judge already — the very Message which I have delivered will itself be his judge at the Last Day.
Akwai mai hukunci saboda wanda ya ƙi ni, bai kuma karɓi kalmomina ba; wannan maganar da na faɗa ita ce za tă hukunta shi a rana ta ƙarshe.
49 For I have not delivered it on my own authority; but the Father, who sent me, has himself given me his command as to what I should say, and what message I should deliver.
Gama ba don kaina na yi magana ba, Uban da ya aiko ni shi kansa ne ya ba ni umarni a kan abin da zan faɗa da kuma yadda zan faɗe shi.
50 And I know that Immortal Life lies in keeping his command. Therefore, whatever I say, I say only what the Father has taught me.” (aiōnios )
Na san cewa umarninsa yana kai ga rai madawwami. Saboda haka duk abin da na faɗa na faɗe shi ne kamar dai yadda Uba ya ce in faɗa.” (aiōnios )