< Hebrews 8 >
1 To sum up what I have been saying: — Such is the High Priest that we have, one who ‘has taken his seat at the right hand’ of the throne of God’s Majesty in Heaven,
Yanzu abin da muke kokarin cewa shine: Muna da babban firist wanda ke zaune a hannun dama na kursiyi mai martaba dake sammai.
2 where he ministers in the Sanctuary, in that true Tabernacle set up by the Lord and not by man.
Shi kuwa bawa ne a wannan wuri mai tsarki, haikali na gaskiya wanda Allah ya shirya ba wani bil'adama ba.
3 Every High Priest is appointed for the purpose of offering gifts and sacrifices to God; it follows, therefore, that this High Priest must have some offering to make.
Kowanne babban firist kuwa yana mika bayebaye da hadayu. Don haka ya kamata a sami abin hadaya.
4 If he were, however, still upon earth, he would not even be a priest, since there are already priests who offer the gifts as the Law directs.
Da a ce Almasihu yana duniya ba zai zama firist ba ko kadan.
5 (These priests, it is true, are engaged in a service which is only a copy and shadow of the heavenly realities, as is shown by the directions given to Moses when he was about to construct the Tabernacle. ‘Look to it,’ are the words, ‘that thou make every part in accordance with the pattern shown thee on the mountain.’)
Domin a kwai masu mika hadaya bisa ga shari'a. Suna hidimar misalin abubuwan da suke inuwar sama. Kamar yadda Allah ya yi wa Musa gargadi yayin da ya ke shirin gina Alfarwa: ''Duba'' Allah ya ce, ''kayi komai bisa ga salon da aka koya maka a bisa dutse.”
6 But Jesus, as we see, has obtained a ministry as far excelling theirs, as the Covenant of which he is the intermediary, based, as it is, on better promises, excels the former Covenant.
Amma yanzu hidimar da Almasihu ya karba ta dara tasu dukka, domin kuwa shine matsakancin muhimmin alkawari, wanda aka kammala a kan muhimman alkawura.
7 If that first Covenant had been faultless, there would have been no occasion for a second.
Domin kuwa idan alkawarin fari ba shi da laifi babu anfanin neman alkawari na biyu.
8 But, finding fault with the people, God says — ‘“Behold, a time is coming,” says the Lord, “When I will ratify a new Covenant with the People of Israel and with the People of Judah —
Da Allah ya sami laifi akan mutane, sai ya ce ''Zan sake sabon alkawari da gidan Isra'ila da kuma gidan Yahuza.
9 Not such a Covenant as I made with their ancestors On the day when I took them by the hand to lead them out of the land of Egypt. For they did not abide by their Covenant with me, And therefore I disregarded them,” says the Lord.
kuma ba zai zama kamar yadda nayi da kakanninku ba, kamar yadda na rike su a hannu har Na fidda su daga kasar Masar. Basu kuma ci gaba da Alkawarina ba, ni kuwa na yi watsi da su,'' inji Ubangiji.
10 “This is the Covenant that I will make with the People of Israel After those days,” says the Lord. “I will impress my laws on their minds, And will inscribe them on their hearts; And I will be their God, And they shall be my People.
Gama wanna shine alkawarin da zan yi da gidan Isra'ila bayan wadannan kwanaki, Inji Ubangiji. Zan sa shari'a ta a bakinsu in kuma rubuta ta a zuciyarsu, Zan kuma zama Allah a garesu, su kuma su zama jama'ata.
11 There shall be no need for every man to instruct his fellow-citizen, Or for a man to say to his Brother ‘Learn to know the Lord’; For every one will know me, From the lowest to the highest.
Ba za su kuma koyar da makwabta ko yan'uwansu cewa, ''ku san Ubangiji'' gama dukkanin su za su san ni, daga karami har zuwa babba.
12 For I will be merciful to their wrong-doings, And I will no longer remember their sins.”’
Zan kuma nuna tausayi ga ayyukan su na rashin adalci, ba kuma zan kara tunawa da zunubansu ba.
13 By speaking of a ‘new’ Covenant, God at once renders the former Covenant obsolete; and whatever becomes obsolete and loses its force is virtually annulled.
A kan fadin ''sabo'' ya mayar da alkawarin fari tsoho. Wannan kuma da aka ambata tsoho na shirin bacewa.