< Acts 18 >

1 On leaving Athens, Paul next went to Corinth.
Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
2 There he met a Jew of the name of Aquila, a native of Pontus, who, with his wife Priscilla, had lately come from Italy, in consequence of the order which had been issued by the Emperor Claudius for all Jews to leave Rome. Paul paid them a visit,
A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
3 and, since their trade was the same as his, he stayed and worked with them — their trade was tent-making.
da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
4 Every Sabbath Paul gave addresses in the Synagogue, trying to convince both Jews and Greeks.
Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
5 But, when Silas and Timothy had come down from Macedonia, Paul devoted himself entirely to delivering the Message, earnestly maintaining before the Jews that Jesus was the Christ.
Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
6 However, as they set themselves against him and became abusive, Paul shook his clothes in protest and said to them: “Your blood be on your own heads. My conscience is clear. From this time forward I shall go to the Gentiles.”
Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
7 So he left, and went to the house of a certain Titius Justus, who had been accustomed to join in the worship of God, and whose house was next door to the Synagogue.
Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
8 Crispus, the President of the Synagogue, came to believe in the Lord, and so did all his household; and many of the Corinthians, as they listened to Paul, became believers in Christ and were baptized.
Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
9 One night the Lord said to Paul, in a vision: “Have no fear, but continue to speak, and refuse to be silenced;
Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
10 for I am with you, and no one shall do you harm, for I have many People in this city.”
Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
11 So he settled there for a year and a half, and taught God’s Message among the people.
Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
12 While Gallio was governor of Greece, the Jews made a combined attack on Paul, and brought him before the Governor’s Bench,
Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
13 charging him with persuading people to worship God in a way forbidden by the Law.
Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
14 Just as Paul was on the point of speaking, Gallio said to the Jews: “Jews, if this were a case of misdemeanour or some serious crime, there would be some reason for my listening patiently to you;
A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
15 but, since it is a dispute about words, and names, and your own Law, you must see to it yourselves. I do not choose to be a judge in such matters.”
Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
16 Saying this, he drove them back from the Bench.
Saboda haka ya kore su.
17 Then they all set upon Sosthenes, the President of the Synagogue, and beat him in front of the Bench, but Gallio did not trouble himself about any of these things.
Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
18 Paul remained there some time after this, and then took leave of the Brethren, and sailed to Syria with Priscilla and Aquila, but not before his head had been shaved at Cenchreae, because he was under a vow.
Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
19 They put into Ephesus, and there Paul, leaving his companions, went into the Synagogue and addressed the Jews.
Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
20 When they asked him to prolong his stay, he declined, saying however,
Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
21 as he took his leave, “I will come back again to you, please God,” and then set sail from Ephesus.
Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
22 On reaching Caesarea, he went up to Jerusalem and exchanged greetings with the Church, and then went down to Antioch.
Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
23 After making some stay in Antioch, he set out on a tour through the Phrygian district of Galatia, strengthening the faith of all the disciples as he went.
Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
24 Meanwhile there had come to Ephesus an Alexandrian Jew, named Apollos, an eloquent man, who was well-versed in the Scriptures.
Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
25 He had been well-instructed in the Cause of the Lord, and with burning zeal he spoke of, and taught carefully, the facts about Jesus, though he knew of no baptism but John’s.
An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
26 This man began to speak out fearlessly in the Synagogue; and when Priscilla and Aquila heard him, they took him home and explained the Cause of God to him more carefully still.
Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
27 When he wanted to cross to Greece, the Brethren furthered his plans, and wrote to the disciples there to welcome him. On his arrival he proved of great assistance to those who had, through the loving-kindness of God, become believers in Christ,
Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
28 for he vigorously confuted the Jews, publicly proving by the Scriptures that Jesus was the Christ.
Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.

< Acts 18 >