< Acts 1 >
1 The first account which I drew up, Theophilus, dealt with all that Jesus did and taught from the very first,
A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
2 down to that day on which he was taken up to Heaven, after he had, by the help of the Holy Spirit, given instructions to the Apostles whom he had chosen.
har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
3 With abundant proofs, he showed himself to them, still living, after his death; appearing to them from time to time during forty days, and speaking of all that related to the Kingdom of God.
Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
4 And once, when he had gathered them together, he charged them not to leave Jerusalem, but to wait there for the fulfilment of the Father’s promise — “that promise,” he said, “of which you have heard me speak;
A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
5 for, while John baptized with water, you shall be baptized with the Holy Spirit before many days have passed.”
Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
6 So, when the Apostles had met together, they asked Jesus this question — “Master, is this the time when you intend to re-establish the Kingdom for Israel?”
Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
7 His answer was: “It is not for you to know times or hours, for the Father has reserved these for his own decision;
Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
8 but you shall receive power, when the Holy Spirit shall have descended upon you, and shall be witnesses for me not only in Jerusalem, but throughout Judea and Samaria, and to the ends of the earth.”
Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
9 No sooner had Jesus said this than he was caught up before their eyes, and a cloud received him from their sight.
Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
10 While they were still gazing up into the heavens, as he went, suddenly two men, clothed in white, stood beside them,
Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
11 and said: “Men of Galilee, why are you standing here looking up into the heavens? This very Jesus, who has been taken from you into the heavens, will come in the very way in which you have seen him go into the heavens.”
Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
12 Then the Apostles returned to Jerusalem from the hill called Olivet, which is about three quarters of a mile from the city.
Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
13 When they reached Jerusalem, they went to the upstairs room, where they were staying. There were there Peter, John, James, and Andrew, Philip and Thomas, Bartholomew and Matthew, James the son of Alphaeus, Simon the Zealot, and Judas the son of James.
Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
14 They all united in devoting themselves to Prayer, and so did some women, and Mary, the mother of Jesus, and his brothers.
Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
15 About this time, at a meeting of the Brethren, when there were about a hundred and twenty present, Peter rose to speak.
A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
16 “Brothers,” he said, “it was necessary that the prediction of Scripture should be fulfilled, which the Holy Spirit made by the lips of David about Judas, who acted as guide to the men that arrested Jesus,
ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
17 for he was one of our number and had his part allotted him in this work of ours.”
dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
18 (This man had bought a piece of land with the price of his treachery; and, falling heavily, his body had burst open, and all his bowels protruded.
(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
19 This became known to every one living in Jerusalem, so that the field came to be called, in their language, ‘Akeldama,’ which means the ‘Field of Blood.’)
Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
20 “For in the Book of Psalms,” Peter continued, “it is said — ‘Let his dwelling become desolate, And let no one live in it’; and also — ‘His office let another take.’
Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
21 Therefore, from among the men who have been with us all the time that Jesus, our Master, went in and out among us —
Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
22 From his baptism by John down to that day on which he was taken from us — some one must be found to join us as a witness of his resurrection.”
farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
23 So they put forward two men, Joseph called Barsabas, whose other name was Justus, and Matthias;
Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
24 and they offered this prayer — “O Lord, who reads all hearts, show which of these two men you have chosen
Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
25 To take the place in this apostolic work, which Judas has abandoned, to go to his proper place.”
ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
26 Then they drew lots between them; and, the lot having fallen on Matthias, he was added to the number of the eleven Apostles.
Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.