< 2 Corinthians 4 >
1 Therefore, since it is by God’s mercy that we are engaged in this ministry, we do not lose heart.
Saboda haka, da yake ta wurin jinƙan Allah ne muke da wannan hidima, ba za mu fid da zuciya ba.
2 No, we have renounced the secrecy prompted by shame, refusing to adopt crafty ways, or to tamper with God’s Message, and commending ourselves to every man’s conscience, in the sight of God, by our exhibition of the Truth.
Ba ruwanmu da ɓoye-ɓoye na munafuncin da suke abubuwan kunya. Ba ruwanmu da ruɗu, ko yin ƙarya da kalmar Allah. Sai dai muna faɗin gaskiya a fili. Ta haka ne kowa zai yi shaidar gaskiyarmu a gaban Allah cikin zuciyarsa.
3 And, even if the Good News that we bring is veiled, it is veiled only in the case of those who are on the path to Ruin —
Ko da bishararmu a rufe take, tana a rufe ne ga waɗanda suke hallaka.
4 Men whose minds have been blinded by the God of this Age, unbelievers as they are, so that the light from the Good News of the glory of the Christ, who is the very incarnation of God, should not shine for them. (aiōn )
Allahn zamanin nan ya makanta hankulan marasa ba da gaskiya, yadda har ba za su iya ganin hasken bishara ta ɗaukakar Kiristi ba, wanda yake kamannin Allah. (aiōn )
5 (For it is not ourselves that we proclaim, but Christ Jesus, as Lord, and ourselves as your servants for Jesus’ sake.)
Gama ba wa’azin kanmu muke yi ba, sai dai na Yesu Kiristi, a kan shi ne Ubangiji, mu kuma bayinku saboda Yesu.
6 Indeed, the same God who said ‘Out of darkness light shall shine,’ has shone in upon our hearts, so that we should bring out into the light the knowledge of the glory of God, seen in the face of Christ.
Domin shi Allah wanda ya ce, “Bari haske yă haskaka daga duhu,” ya sa haskensa ya haskaka a cikin zukatanmu, don yă ba mu hasken sanin ɗaukakar Allah a fuskar Kiristi.
7 This treasure we have in these earthen vessels, that its all-prevailing power may be seen to come from God, and not to be our own.
Amma muna da wannan dukiya a cikin tulunan yumɓu, don a nuna wannan mafificin ikon nan daga Allah ne, ba daga gare mu ba.
8 Though hard pressed on every side, we are never hemmed in; through perplexed, never driven to despair;
A matse muke a kowane gefe, sai dai ba a gurgunta mu ba. An rikitar da mu, amma ba mu fid da zuciya ba.
9 though pursued, never abandoned; though struck down, never killed!
An tsananta mana, amma ba a yashe mu ba, an fyaɗe mu da ƙasa, amma ba a hallaka mu ba.
10 We always bear on our bodies the marks of the death that Jesus died, so that the Life also of Jesus may be exhibited in our bodies.
Kullum muna ɗauke da mutuwar Yesu a jikinmu, domin ran Yesu yă bayyana a jikinmu.
11 Indeed, we who still live are continually being given over to death for Jesus’ sake, so that the Life also of Jesus may be exhibited in our mortal nature.
Muddin muna a raye, kullum zaman mutuwa muke yi saboda Yesu, don a bayyana ran Yesu ta wurin jikin nan namu mai mutuwa.
12 And so, while death is at work within us, Life is at work within you.
Ta haka, mutuwa tana aiki a cikinmu, ku kuwa rai a cikinku.
13 But, in the same spirit of faith as that expressed in the words — ‘I believed, and therefore I spoke,’ we, also believe, and therefore speak.
A rubuce yake cewa, “Na gaskata; saboda haka na yi magana.” Da wannan ruhun bangaskiya ne mu ma muka gaskata, saboda haka muke magana.
14 For we know that he who raised the Lord Jesus will raise us also with him, and will bring us, with you, into his presence.
Domin mun san cewa shi da ya tā da Ubangiji Yesu daga matattu, zai tashe mu mu ma tare da Kiristi, yă kuma miƙa mu a gabansa tare da ku.
15 For all this is for your sakes, that the loving-kindness of God, spreading from heart to heart, may cause yet more hearts to overflow with thanksgiving, to his glory.
Duk wannan fa don amfaninku ne, domin alherin nan da yake bazuwa zuwa ga mutane masu yawa, yă zama dalilin godiya mai yawa ga ɗaukakar Allah.
16 Therefore, as I said, we do not lose heart. No, even though outwardly we are wasting away, yet inwardly we are being renewed day by day.
Saboda haka, ba mu fid da zuciya ba. Ko da yake a waje, jikinmu mai mutuwa yana lalacewa, amma can ciki, ana sabunta mu kowace rana.
17 The light burden of our momentary trouble is preparing for us, in measure transcending thought, a weight of imperishable glory; (aiōnios )
Don wannan’yar wahalar tamu mai saurin wucewa, ita take tanadar mana madawwamiyar ɗaukaka mai yawa, fiye da kwatanci. (aiōnios )
18 we, all the while, gazing not on what is seen, but on what is unseen; for what is seen is transient, but what is unseen is imperishable. (aiōnios )
Domin ba abubuwan da ido yake gani ne muke dubawa ba, sai dai marasa ganuwa. Gama abubuwan da ake gani masu saurin wucewa ne, marasa ganuwa kuwa, madawwama ne. (aiōnios )