< 1 Corinthians 1 >
1 To the Church of God in Corinth, to those who have been consecrated by union with Christ Jesus and called to become his People, and also to all, wherever they may be, who invoke the Name of our Lord Jesus Christ — their Master and ours,
Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
2 from Paul, who has been called to be an Apostle of Jesus Christ by the will of God, and from Sosthenes, our Brother.
Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
3 May God, our Father, and the Lord Jesus Christ bless you and give you peace.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 I always thank God about you for the blessing bestowed upon you in Christ Jesus.
Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
5 For through union with him you were enriched in every way — in your power to preach, and in your knowledge of the Truth;
Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
6 and so became yourselves a confirmation of my testimony to the Christ.
gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
7 And thus there is no gift in which you are deficient, while waiting for the Appearing of our Lord Jesus Christ.
Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
8 And God himself will strengthen you to the end, so that at the Day of our Lord Jesus Christ you may be found blameless.
Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 God will not fail you, and it is he who called you into communion with his Son, Jesus Christ, our Lord.
Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
10 But I appeal to you, Brothers, by the Name of our Lord Jesus Christ, to agree in what you profess, and not to allow divisions to exist among you, but to be united — of one mind and of one opinion.
Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
11 For I have been informed, my Brothers, by the members of Chloe’s household, that party feeling exists among you.
’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
12 I mean this: that every one of you says either ‘I follow Paul,’ or ‘I Apollos,’ or ‘I Kephas,’ or ‘I Christ.’
Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
13 You have rent the Christ in pieces! Was it Paul who was crucified for you? or were you baptized into the Faith of Paul?
Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
14 I am thankful that I did not baptize any of you except Crispus and Gaius,
Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
15 so that no one can say that you were baptized into my Faith.
Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
16 I baptized also the household of Stephanas. I do not know that I baptized any one else.
(I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
17 My mission from Christ was not to baptize, but to tell the Good News; not, however, in the language of philosophy, lest the cross of the Christ should be robbed of its meaning.
Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
18 The Message of the Cross is indeed mere folly to those who are in the path to Ruin, but to us who are in the path of Salvation it is the very power of God.
Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
19 For Scripture says — ‘I will bring the philosophy of the philosophers to nought, and the shrewdness of the shrewd I will make of no account.’
Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
20 Where is the Philosopher? where the Teacher of the Law? where the Disputant of to-day? Has not God shown the world’s philosophy to be folly? (aiōn )
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
21 For since the world, in God’s wisdom, did not by its philosophy learn to know God, God saw fit, by the ‘folly’ of our proclamation, to save those who believe in Christ!
Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
22 While Jews ask for miraculous signs, and Greeks study philosophy,
Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
23 we are proclaiming Christ crucified! — to the Jews an obstacle, to the Gentiles mere folly,
amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
24 but to those who have received the Call, whether Jews or Greeks, Christ, the Power of God and the Wisdom of God!
amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
25 For God’s ‘folly’ is wiser than men, and God’s ‘weakness’ is stronger than men.
Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
26 Look at the facts of your Call, Brothers. There are not many among you who are wise, as men reckon wisdom, not many who are influential, not many who are high-born;
’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
27 but God chose what the world counts foolish to put its wise men to shame, and God chose what the world counts weak to put its strong things to shame,
Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
28 and God chose what the world counts poor and insignificant — things that to it are unreal — to bring its ‘realities’ to nothing,
Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
29 so that in his presence no human being should boast.
domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
30 But you, by your union with Christ Jesus, belong to God; and Christ, by God’s will, became not only our Wisdom, but also our Righteousness, Holiness, and Deliverance,
Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
31 so that — in the words of Scripture — ‘Let him who boasts make his boast of the Lord!’
Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”