< Zechariah 8 >

1 Yahweh gave me [another] message. He said,
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
2 “This is what [I], the Commander of the armies of angels, say: ‘I love [the people of] Jerusalem; I love them very much, and I am very angry with their enemies.’
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
3 So this is what I say: ‘[Some day] I will return to Zion [Hill] and I will live there. [At that time, ] Jerusalem will be called the city [where people] (are faithful to/faithfully obey) me, and [people will say that Zion] Hill [is] holy because it is where the Commander of the armies of angels dwells.’”
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
4 The Commander of the armies of angels also says this: “[Some day] old men and old women will again sit along the streets of Jerusalem, each of them holding a cane because of their being very old.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
5 And the city streets with be full of boys and girls playing.”
Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
6 The Commander of the armies of angels [also] says this: “[When those things happen, ] it will seem marvelous to the people who are still alive, but it certainly will not [RHQ] seem marvelous to me!”
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
7 The Commander of the armies of angels [also] says this: “I will rescue my people from countries to the northeast and to the southwest [to which they were forced to go].
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
8 I will bring them back [to Judah], and they will [again] live in Jerusalem. They will be my people, and I will be their God. I will be faithful [to them] and act righteously [toward them].”
Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
9 The Commander of the armies of angels [also] says this: “When the foundation for my temple was laid, there were prophets there who proclaimed messages [from me]. Some of you heard what those prophets said. [So] be brave/courageous [MTY] [while you are building] the temple, in order that you may [finish] building it.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
10 Before [you started to rebuild the temple], [no one could hire] men or animals [to work for them, because] there was no money to pay for them. And people were afraid to go anywhere because I had caused people to oppose each other, and [they thought that] there were enemies [everywhere].
Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
11 But now I will act differently toward [you] people who are still alive, [differently] than I did previously. [That is what I], the Commander of the armies of angels, say.
Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 [From now on, ] it will be peaceful when you plant [your seeds], and your grapevines will produce grapes, and good crops will grow in your fields. There will be rain. I will give all those things to [you] people who are still alive.
“Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
13 You [people of] Judah and Israel, [the people of other] nations have cursed you. But I will rescue you, and you will be a blessing [to the people of many nations. So] do not be afraid; work hard [MTY] [to finish building the temple].”
Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
14 The Commander of the armies of angels [also] says this: “When your ancestors caused me to become very angry, I decided to punish them. And I did not change my mind.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
15 But now [I will do something different]. I am planning to do good things to [the people of] Jerusalem and [other towns in] Judah. [So] do not be afraid.
kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
16 These are the things that you should do: [You should always] tell the truth to each other. In the courts, [your judges must] make decisions according to what is correct and fair.
Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
17 Do not plan to do evil things to others, and do not falsely promise [to do things that you know that you will not do]. I hate all those things.”
kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
18 The Commander of the armies of angels spoke to me [again].
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
19 This is what he said: “The times when you people of Judah (fast/abstain from food) during the fourth, fifth, seventh, and tenth months [of each year] will become good and very happy/joyful [DOU] festivals. But you must want [to speak] truthfully and [be] peaceful.”
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
20 The Commander of the armies of angels [also] says this: “[Some day] people from many [people-groups and foreign] cities will come [here to Jerusalem].
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
21 People from one city will go to [the people in] another [city] and say, ‘Let’s [go together to Jerusalem] to worship Yahweh and ask him to bless us; we [ourselves] are going.’
mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
22 And [people from] many people-groups and [from] powerful nations will come to Jerusalem to worship Yahweh and ask him to bless them.”
Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
23 The Commander of the armies of angels [also] says this: “At that time, [this is what will happen everywhere]: A group of people from one nation or a group of people who speak another language will grab the fringe/edge of the robe of a Jew and say [to him], ‘We have heard [people say] that God is with you. So allow us to go with you [to Jerusalem to worship him].’”
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”

< Zechariah 8 >