< Zechariah 4 >
1 Then the angel who had been talking with me returned, and he called to me as though I had been asleep.
Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
2 He asked me, “What do you see?” I replied, “I see a lampstand [made] completely of gold. There is a small bowl [for olive oil] at the top, and there are seven [small] lamps around the bowl, and a place for a wick on each lamp.
Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
3 Furthermore, I see two olive trees, one at the right side of the lampstand and one at the left side.”
Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
4 I asked the angel who was talking with me, “Sir, what are these?”
Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
5 He replied, “Surely you know [RHQ] what they are?” I replied, “No, I do not know.”
Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
6 Then he said to me, “This is the message that Yahweh [says that you should give] to Zerubbabel [the governor of Judah: ‘You will do what I want you to do, but it will] not be by your own strength or power. It will be [done] by [the power of] my Spirit, says the Commander of the armies of angels.
Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
7 Zerubbabel, you [have many difficult matters to handle. They are like] high mountains [MET]. But they will [become easy to handle, as though] they will become flat land. And you will bring [to the temple] the final stone [to complete the rebuilding of the temple]. When you do that, [all the people] will shout repeatedly, “It is beautiful! May God bless it!”’”
“Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
8 Then Yahweh gave me [another] message.
Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
9 He said [to me], “Zerubbabel [SYN] laid the first stone in the foundation of the temple, and he will put the last stone in its place. When that happens, the people will know that [it is I, the Commander of the armies of angels, who] have sent you to them.” And he said, “The seven bowls represent the eyes of Yahweh, who looks back and forth at everything [that happens] on the earth.”
“Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
10 No one [RHQ] should think that little things that are done at the beginning of a big project are unimportant. [When the temple is almost finished being rebuilt, ] Zerubbabel will use a (plumb line/string with a stone fastened to it) [to see if the walls they are building are straight]; so when the people see that, they will rejoice.”
“Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
11 Then I asked the angel, “What is [the meaning of] the two olive trees, one on each side of the lampstand?
Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
12 And what [the meaning of] the two olive branches, one alongside each of the gold pipes from which [olive] oil flows to the lamps?”
Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
13 He replied, “Surely [RHQ] you know what they are?” I replied, “No, sir, [I do not know.]”
Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
14 So he said, “They represent the two [men who have been] appointed [MTY] to serve the Lord who [rules] the entire earth.”
Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”