< Zechariah 14 >
1 Listen! It will soon be the time when Yahweh [will judge everyone]. At that time, the possessions that were taken from you [people of Jerusalem by your enemies will be returned to you, and] will be divided among you.
Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
2 [Before that happens, ] Yahweh will cause [the armies of] many [HYP] nations to attack Jerusalem. They will capture the city and steal all the valuable things from your houses and rape the women. They will take half of the people to other countries, but the other half of the people will be allowed to remain in the city.
Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
3 Then Yahweh will go out to fight against those nations; he will fight like [SIM] [soldiers] fight in a battle.
Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
4 On that day, he will stand on Olive [Tree] Hill, east of Jerusalem. Olive [Tree] Hill will be split into two [parts], with a large valley between the parts. Half of the hill will move toward the north and half [will move] toward the south.
A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
5 People will flee through that valley which extends to the other side (OR, to Azel), like [SIM] people fled when there was an earthquake during the time that King Uzziah ruled Judah. Then Yahweh my God will come with his holy [angels].
Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
6 At that time, there will be no light [from the sun]; it will not become cold and there will be no frost.
A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
7 There has been no other time like that time, and only Yahweh knows when it will happen. There will be no daytime or nighttime; there will be [light continually], [even] in the evening.
Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
8 At that time, running/fresh water will flow from Jerusalem. One stream will flow toward the east to the [Dead] Sea. The other stream will flow toward the west to the [Mediterranean] Sea. The water will flow [all the time], during (summer/the hot season) as well as in (winter/the cold season).
A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
9 After that time, Yahweh will be the king [who rules] the entire world. [Everyone will know that] Yahweh, and only Yahweh [MTY], is the true God.
Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
10 [At that time, ] all the land [in Judah] from Geba [town at the north] to Rimmon [town far to] the south of Jerusalem, will become a plain. Jerusalem will remain raised up like it has always been. [It will extend] from the Benjamin Gate and the First Gate [northeast] to the Tower of Hananel, and to the king’s winepresses [to the southwest].
Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
11 Many people will live there, and the city will never be destroyed again. It will be a safe city.
Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
12 But Yahweh will cause the people in all the nations that attacked Jerusalem to be afflicted by a (plague/severe illness). Their flesh will rot while they are still standing up. Their eyes will rot in their sockets and their tongues will rot in their mouths.
Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
13 At that time, Yahweh will cause many people to panic. People will grab and attack each other.
A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
14 [The people who live in other places in] Judah will fight to defend Jerusalem. They will collect the valuable things from the surrounding nations—a lot of gold and silver and clothes.
Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
15 The same plague [that will afflict the people of other nations] will afflict their horses, mules, camels, donkeys, and all the other work animals in their (camps/places where they have set up their tents).
Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
16 The people of other nations who [previously] came [to fight] against Jerusalem, all those who are still alive, will return to Jerusalem every year to worship the King, the Commander of the armies of angels, and to celebrate the Festival of Living in Temporary Shelters.
Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
17 If there are people in those nations who do not go [to Jerusalem to worship there], rain will not fall on their land.
In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
18 If the people of Egypt [or any other nation] do not go to Jerusalem, [they will not have any rain]. And Yahweh will cause them to experience the same plague that afflicted the [people of other] nations that did not celebrate the Festival of Living in Temporary Shelters.
In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
19 That is how [Yahweh] will punish [the people of] Egypt and [the people of] any [other] nation who do not go [to Jerusalem] to celebrate the Festival of Living in Temporary Shelters.
Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
20 At that time, [the words] ‘Dedicated to Yahweh’ will be written on the bells that are fastened to the horses. The [cooking] pots in [the courtyard of the] temple will be [sacred], like the bowls that are near the altar.
A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
21 Every pot in Jerusalem and [in other places in] Judah will be dedicated to the Commander of the armies of angels. So everyone who offers sacrifices [there in Jerusalem] will be able to take some of the meat that has been brought for sacrifices, and cook it in their own pots. And at that time, people will no longer buy or sell things in [the courtyard of] the temple of the Commander of the armies of angels.
Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.