< Ruth 1 >

1 During the time before kings ruled Israel, (there was a famine/the people there had nothing to eat). There was a man who lived there whose name was Elimelech. His wife’s name was Naomi, and his sons’ names were Mahlon and Chilion. They were all from Bethlehem [town], from the Ephrath [clan] in Judah [region].
A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
2 Because of the famine, they left Bethlehem and went east to [live for a while in] Moab [region].
Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
3 While they were there, Elimelech died, and Naomi had only her two sons with her.
To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
4 They married women from Moab. One of them was named Orpah, and the other one was named Ruth. But after they had lived in that area for about ten years,
Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
5 Mahlon and Chilion died. So then Naomi had no husband and no sons.
sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
6 One day while Naomi was in Moab, she heard someone say that Yahweh had helped his people in Israel and that now there was plenty of food to eat. So she prepared to return [to Bethlehem].
Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
7 She left the place where she had been living and started to walk [with her daughters-in-law] along the road back to Judah.
Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
8 Then as the three of them were walking, Naomi said to her two daughters-in-law, “Each of you should turn around and go back to your mother’s home. You treated [your husbands] kindly [before] they died, and you have treated me kindly.
Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
9 Now I desire that Yahweh will enable each of you to have another husband in whose home you will [feel] secure.” Then she kissed both of them, and they cried aloud.
Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
10 They each said, “No, we want to go with you as you return to your relatives.”
suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
11 But Naomi said, “No, my daughters, return home. (It will not do any good for you to come with me!/What good will it do for you to come with me?) [RHQ] Do you think I will get married again and have more sons who could become your husbands?
Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
12 Even if I thought I could have another husband, and even if I got married today and became pregnant [EUP] tonight and later gave birth to sons,
Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
13 would you remain single/unmarried until they grew up [and became old enough] for you to marry? No, my daughters, [you would not do that]. Your situations are bad [because your husbands have died, but it is possible that you will each marry again]. My situation is much worse, because Yahweh [SYN] has opposed me, [and now I am too old to get married again].”
za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
14 Then Ruth and Orpah cried again [because of what Naomi said]. Then Orpah kissed her mother-in-law goodbye, [and left], but Ruth clung to Naomi.
A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
15 Naomi said to her, “Look! Your sister-in-law is going back to her relatives and to her gods! Go back with her!”
Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
16 But Ruth replied, “No! Don’t urge me to leave you! I [want to] go with you. Where you go, I will go. Where you stay, I will stay. Your relatives will be my relatives, and the God you [worship] will be the God I [worship].
Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
17 Where you die, I will die. Where you are buried, I will be buried. May Yahweh punish me severely if I separate from you. I will be separated from you only [when one of us] dies.”
Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
18 When Naomi realized that Ruth was very determined to go with her, she stopped urging her [to return home].
Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
19 So the two women continued walking until they came to Bethlehem. When they arrived there, everyone in town was excited [to see] them. The women [of the town] exclaimed, “(Can this be Naomi?/It is difficult to believe that this is Naomi!)” [RHQ]
Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
20 Naomi said to them, “Don’t call me Naomi, [which means ‘pleasant’]. Instead, call me Mara, [which means ‘bitter’], because God Almighty has made my life very unpleasant.
Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
21 When I left here, I [felt] rich, [because I had a family]. But Yahweh has brought me back here and now I [feel] poor, [because I have no family]. Do not call me Naomi [RHQ]. [I feel as though] Yahweh has spoken against (OR, afflicted) me. Almighty [God] has caused me to experience a great tragedy.”
In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
22 That [summarizes the account] of Naomi returning home along with her daughter-in-law Ruth, the woman from Moab. And [it happened that] when they arrived in Bethlehem, the barley [grain] harvest was just beginning.
Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.

< Ruth 1 >