< Revelation 1 >

1 [This book tells the message] that God revealed to Jesus Christ. God revealed it to him in order that he might reveal to his servants the [things/events] that must happen soon. Jesus communicated [this message] to [me], his servant John, by sending his angel to me.
Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya.
2 [As I write it, I], John, am truthfully reporting everything that I saw [and heard], the message from God that Jesus Christ [truthfully reported to me].
Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu.
3 [God is] pleased with those who read [this book to the congregations], and he will be pleased with those who listen carefully to it and obey what [he has commanded in this prophetic message that I] am writing. [So read this message to the congregations, listen carefully to it, and obey it], because [these things that Jesus has revealed] will happen soon.
Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.
4 [I], John, am [writing this] to [you believers in] the seven congregations [that are located] in Asia [province]. [I pray that God the Father, God’s Spirit, and Jesus Christ] be kind to (OR, bless) you and cause you to have [inner] peace. [God the Father is] the one who exists, who has always existed, and who will always exist. The Spirit [of God, who] is in front of God’s throne, has [all kinds of power] (OR, The Spirit of God [is symbolized] by seven spirits who are in front of God’s throne).
Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa,
5 Jesus Christ is the one who has faithfully told [people about God]. He is the first one (whom God has raised from the dead/who became alive again after being dead), in order [to show that God will raise us who trust in Jesus]. Jesus is the one who rules the kings of the earth. He is the one who loves us. He is the one who has erased the record our sins. He did that by shedding his blood [when he died on the cross].
kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa,
6 He is [the one who] has caused us to become people whose lives God rules, and he has made us to be priests [who serve] God his Father. [As a result of this, we acknowledge that] Jesus Christ is eternally divine and eternally powerful. (Amen!/That is true!) (aiōn g165)
ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin. (aiōn g165)
7 Listen carefully! Christ will surely come in the midst of the clouds [in order that he may judge the rebellious people of earth], and everyone [SYN] will see him [come]. Even those who [are responsible for] piercing [and killing] him [MTY] [will see him come. People from] all people-groups on earth will mourn because he [will punish them]. (Amen!/May it be so.)
Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin.
8 The Lord God declares, “I am the one who created [everything], and I am the [one who will cause everything to] end [MET].” He is the one who exists, who has always existed, and who will always exist. He is the Almighty One.
“Nine na farko da na karshe”, in ji Ubangiji Allah, “Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka.”
9 I, John, your fellow believer, am suffering as you [are] because of our letting Jesus rule [our lives]. We are steadfastly enduring [trials] because of our relationship with him. I was punished by being sent/exiled to Patmos island because [of my proclaiming] God’s message and telling [people about] Jesus.
Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu.
10 [God’s] Spirit took control of me on one of the days [that we believers met to worship] the Lord.
Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho.
11 [At that time], I heard behind me someone [speaking to me as loudly and as clearly] [SIM] as a trumpet. He was saying [to me], “Write on a scroll what you see, and send it to seven congregations. Send it to [the congregations] in Ephesus [city], in Smyrna [city], in Pergamum [city], in Thyatira [city], in Sardis [city], in Philadelphia [city], and in Laodicea [city].”
Ta ce, “Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya.”
12 [In this vision] I turned in order that I might see who had spoken to me [SYN]. When I turned,
Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su
13 I saw seven golden lampstands. In the midst of the lampstands there was [someone] who looked like he came from heaven. He wore a robe that reached to his feet, and he wore a gold band around his chest.
A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
14 The hair on his head was white like white wool [or] like snow. His eyes were [shining brightly] [SIM], like a flame of fire.
Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta.
15 His feet [looked] like brass that glows [as it is being] purified {as [people] purify it} in a furnace. [When he spoke], his voice [sounded] like the sound [made by] a huge waterfall (OR, a great/wide river of rushing water).
Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne.
16 In his right hand he held seven stars. A sword that had two sharp edges extended from his mouth. His face [shone as bright] as the sun shines [at midday] [MTY].
A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
17 When I saw him, I fell down at his feet [and was unable to move or speak] [SIM], as though [I were] dead. But he put his right hand on me and said to me, “Don’t be afraid! I am the one who created [all things] and the [one who will cause all things to] end.
Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe,
18 I am the living one. Although I died, I am alive again and will live forever! I have [the power to cause people] to die, and I have authority over the place where all the dead people [are]. (aiōn g165, Hadēs g86)
da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
19 So write the [vision] that you are seeing. Write about the [conditions] that exist now, and the [events] that are about to happen next.
Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan.
20 The meaning of the seven stars that you saw in my right hand and the seven golden lampstands [that you saw is this]: The seven stars [in my hand represent the leaders, who are like] angels, [who watch over] the seven congregations, and the [seven] lampstands [represent] the seven congregations.”
Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.

< Revelation 1 >