< Revelation 8 >
1 When [Jesus], the [one who is like a] lamb, opened the seventh seal, there was no sound at all in heaven for (a very short time/about half an hour).
Lokacin da Dan Ragon nan ya bude hatimi na bakwai, sai aka yi shiru a sama na kimanin rabin sa'a.
2 I saw the seven angels who stand in front of God. A trumpet was given {([God/An angel]) gave a trumpet} to each one of them.
Sa'anan na ga mala'iku bakwai wadanda ke tsaye a gaban Allah, aka kuma basu kahonni bakwai
3 Another angel, who had a golden container for burning incense, came and stood at the altar. [He was given] {[An angel] gave to him} a large quantity of incense, in order that he might offer it, with the prayers of all God’s people, upon the golden altar that is in front of [God’s] throne. [Then he burned this incense on the altar].
Wani mala'ika ya zo, rike da tasar turaren konawa na zinariya, a tsaye gaban bagadi. Turaren konawa mai yawa aka bashi saboda ya mika su tare da adu'o'in dukan masu bada gaskiya akan bagadin kona turare na zinariya a gaban kursiyin.
4 From the [pot in] the angel’s hand, the smoke of the incense, along with the prayers of God’s people, went up to God.
Hayakin turaren konawa, da adu'o'in masu bada gaskiya, suka tashi sama a gaban Allah daga hanun mala'ikar.
5 [In response], the angel took the golden incense burner and filled it with [coals of] fire from the altar. He threw [the contents of] the [MTY] incense burner onto the earth. Thunder sounded and rumbled, lightning was flashing, and the earth shook.
Mala'ikan ya dauki tasar turaren konawa ya cika ta da wuta daga bagadin. Sa'annan ya wurgo ta kasa zuwa duniya, sai ga tsawar aradu, da cida, da walkiya mai haske, da kuma girgizar kasa.
6 The seven angels, [each] of which had [one of] the seven trumpets, prepared to blow them.
Mala'ikun nan bakwai wadanda suke da kahonni bakwai suka yi shirin busa su.
7 When the first angel blew his trumpet, hail and fire mixed with blood poured down onto the earth. [As a result], a third of [everything on the surface of] the land was burned up {[the fire] burned up a third of [everything on the surface of] the land}. A third of the trees were also burned up {It also burned up a third of the trees}, and [a third of] all the green grass was burned up.
Mala'ika na fari ya hura kahonsa, sai ga kankara da wuta a garwaye da jini. Aka jeho shi kasa zuwa duniya sai kashi daya cikin uku na duniya ya kone, daya cikin uku na itatuwa suka kone, da duk danyar ciyawa suka kone kaf.
8 When the second angel blew his trumpet, something that was like a huge burning mountain fell into the ocean. [As a result], a third of the ocean became [red like] [MTY] blood,
Mala'ika na biyu ya busa kahonsa, sai wani abu mai kama da babban dutse mai cin wuta aka jefo shi cikin teku. Kashi daya cikin uku na tekun ya zama jini,
9 a third of the living creatures in the ocean died, and a third of the ships [in the ocean] were destroyed.
daya cikin uku na rayayyun halittu da ke cikin ruwa suka mutu, sai daya bisa uku na jiragen ruwa aka hallaka.
10 When the third angel blew his trumpet, a huge star, which was burning like a torch, fell from the sky into a third of the rivers and into [a third of] the springs.
Mala'ika na uku ya busa kahonsa, sai gagarumin tauraro ya fado daga sama, yana ci kamar cocila, bisa kashi daya cikin uku na koguna da mabulbulan ruwa.
11 The name of the star is Bitterness. [As a result], the water in a third [of the rivers and springs] became bitter, and many people died from [drinking] the water because it had become bitter.
Sunan tauraron Daci. Kashi daya cikin uku na ruwaye suka yi daci, sai jama'a da yawa suka mutu domin ruwayen sun yi daci.
12 When the fourth angel blew his trumpet, [God] struck the sun, the moon, and the stars, so that they lost a third of their light. The [sun] also did not shine during a third of the day, and [the moon and stars did not shine during a third] of the night.
Mala'ika na hudu ya busa kahonsa, sai daya cikin kashi uku na rana ya harbu, da daya cikin kashi uku na wata da kuma daya cikin kashi uku na taurari. Sai daya cikin kashi uku nasu duka suka duhunce; daya cikin kashi uku na yini da daya cikin uku na dare suka rasa hasken su.
13 As I watched, I heard an eagle that was flying high in the sky, shouting in a loud voice, “Terrible things will happen to [rebellious] people who live on the earth! Terrible things will happen when the three remaining angels blow their trumpets! And they are about to blow them!”
Da na duba sai na ji gaggafa da take shawagi a tsakiyar sararin sama tana kira da babban murya, “Kaito, kaito, kaito, ga mazaunan duniya sabili da sauran karar kahonni na mala'ikun nan uku da za su busa.”