< Psalms 95 >
1 Come, sing to Yahweh; sing joyfully to the one who protects us [MET] and saves us!
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 We should thank him as we come before him, and sing (joyful songs/joyfully) as we praise him.
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 Because Yahweh is the great God, he is a great king [who rules] over all [other] gods.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 He rules over the whole earth, from the deepest places/caves to the highest mountains.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 The seas are his, because he made them. He is [also] the one who [SYN] formed/made the dry land.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 We should come, worship, and bow down before him. We should kneel before Yahweh, the one who made us.
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 He is our God, and we are the people whom he takes care of [MET]; like sheep [that a shepherd] takes care of. Today, listen to what Yahweh is saying to you.
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 He says, “Do not become stubborn [IDM] like [your ancestors] did at Meribah, and like [they did] at Massah in the desert.
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 There your ancestors (wanted to see/tried to determine) if they could do many very evil things [without my punishing them]. Even though they had seen me perform [many] miracles, they tested whether I [would continue to be patient with them].
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 For 40 years I was angry with those people, and I said, ‘Those people say that they want to please me, but they do things that I detest. They refuse to obey my commands.’
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 So because I was very angry, I solemnly said/declared about them: ‘They will never enter [the land of Canaan] where I would have allowed them to rest!’”
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”