< Psalms 82 >
1 God gathers all the [rulers and judges who think they are] gods for a meeting in heaven; and he tells them that he has decided this:
Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
2 “You must [RHQ] stop judging [people] unfairly; you must no longer make decisions that favor wicked [people]!
“Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
3 You must defend [people who are] poor and orphans; you must act fairly toward those who are needy and those who have no one to help them.
Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
4 Rescue them from the power [MTY] of evil [people] [DOU]!”
Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
5 [Those rulers] do not know or understand anything! They are very corrupt/evil, and [as a result of their corrupt/evil behavior], [it is as though] the foundation of the world is being shaken!
“Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
6 I [the all-powerful God, previously] said to them, “You think you are gods! [It is as though] you are all my sons,
“Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
7 but you will die like people do; your lives will end, like the lives of all rulers end.”
Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
8 God, arise and judge [everyone on] [MTY] the earth, because all the people-groups belong to you!
Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.