< Psalms 68 >

1 God, arise and scatter your enemies, and cause those who hate you to run away from you.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 Like [wind] blows smoke away, chase your enemies away. Like wax melts when it is near a fire, cause wicked people to (disappear/be destroyed).
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 But righteous people should be joyful; they should rejoice when they are in God’s presence; they should be happy, and be very joyful.
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Sing to God; sing to praise him; sing a song (OR, make a road) for him who rides on the clouds; his name is Yahweh; be glad when you are in his presence.
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 God, who lives in his sacred temple, is [like] [MET] a father to [those who are] orphans, and he is the one who protects widows.
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 For those who have no one to live with, he provides families [to live with]. He frees prisoners and enables them to be successful, but those who rebel [against him] will be forced to live in a very hot and dry land.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 God, you led your people out [of Egypt], and then you marched with them through the desert.
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 After you did that, because when you, the God [worshiped by us] Israeli people, appeared to us at Sinai [Mountain], the earth shook, and rain poured down from the sky.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 You caused plenty of rain to fall [on your land], [and so] you enabled good crops to grow again on the land that you gave [to us Israelis].
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Your people built homes there; and because you were good to them, you provided [food] for those who were poor.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 The Lord gave a message, and many women took that message to other places.
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 [They proclaimed], “Many kings and their armies are running away [from our army]!” [When our army brought back to their homes] the things that they captured, the women who were at home divided up those things [among themselves and among their families].
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 Even those women who were in the pens [taking care of] the sheep [received some of those things]; they got statues of doves whose wings were covered with silver and whose feathers were covered with pure yellow gold.
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 When Almighty [God] scattered the [enemy] kings [and their armies], [the number of weapons that they abandoned there] seemed like there had been a snowstorm on Zalmon (OR, a black) [Mountain].
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 There is a very high mountain in the Bashan [region], a mountain which has many peaks.
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 But the [people who live near] that mountain should not [RHQ] envy those who live near [Zion], the mountain on which God chose to live! Yahweh will live there forever!
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 [After we defeated all our enemies], [it was as though] the Lord, surrounded by many thousands of strong chariots, descended from Sinai [Mountain] and came into the sacred temple [in Jerusalem].
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 He ascended the sacred mountain [where his temple is], and took with him many people who had been captured [in battles]; and received gifts from the enemies [whom he had defeated]. He received gifts even from those who had rebelled against him, and Yahweh our God will live there [in his sacred temple] forever.
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Praise the Lord, who [helps us] carry our heavy loads every day; he is the one who saves/rescues us.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 Our God is the God who saves us; He is Yahweh, our Lord, the one who (allows us to escape/prevents us) from being killed [in battles].
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 But God will smash the heads of his enemies, the skulls of those who continue to behave sinfully.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 The Lord said, “I will bring back the [corpses of those who were killed in] Bashan, and I will bring back those who sank deep in the ocean [and drowned].
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 I will do that in order that you may wash your feet in their blood, and your dogs can [also] lap up some of your enemies’ blood.”
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 God, many people see you march triumphantly into your sacred temple, [celebrating that you have defeated your enemies]. You [march like] a king does, and a large crowd walks with you.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 The singers are in front, and the people who play stringed instruments are at the rear, and young women who are beating their tambourines are between them.
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 [They are all singing], “You Israeli people, praise God when you gather together; praise Yahweh, all you who are descendants of Jacob!”
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 First come [the people of the tribe of] Benjamin, the smallest [tribe], and following them come the leaders of [the tribe of] Judah and their group, and following them come the leaders of [the tribes of] Zebulun and Naphtali.
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 God, show people that you are very powerful; show people the power with which you have helped us previously.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 Show that power from your temple in Jerusalem, where kings bring gifts to you.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Rebuke [your enemies, such as those in Egypt who are like] wild hippopotamuses/animals that live in the reeds; and [powerful nations that are like] bulls that are among their calves [MET]; rebuke/trample them until they bow down and give you gifts of silver. Scatter the people who enjoy making wars.
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 Then people will bring gifts of bronze (OR, of cloth) to you from Egypt; the people in Ethiopia will lift up their hands [to praise you].
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 [You people who are citizens of] kingdoms/countries all over the world, sing to God! Sing praises to the Lord!
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 Sing to the God, the one who rides across the sky, the sky that [he created] long ago. Listen as he shouts with a very powerful voice.
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 Proclaim that God is very powerful; he is the king that rules over Israel, and in the skies [he also shows that] he is powerful.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 God is awesome as he comes out of his sacred temple; he is the God whom [we] Israeli people [worship]. He makes [DOU] his people very powerful. Praise God!
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!

< Psalms 68 >