< Psalms 64 >
1 God, listen to me as I tell you the things that I am worried about. I am afraid of my enemies; so save/rescue me from them.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
2 Protect me from what wicked men are planning to do to me; protect me from that gang of men who do what is evil.
Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
3 The hostile things they say [MTY] are like [SIM] [sharp] swords; their cruel words are like [SIM] arrows.
Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
4 Without being afraid, they [lie about people and slander people] who have not done what is wrong, like someone who suddenly jumps up from where he is hiding and shoots [arrows] at his enemy [MET].
Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
5 They encourage each other about doing the evil things that they are planning to do; they talk [with each other] about where they can set traps to catch people, and they think, “No one [RHQ] will see what we are doing,
Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
6 because we have planned very well the crime that we are going to commit!” No one can fully understand what people can think and plan!
Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
7 But [it will be as though] God will shoot his arrows at them, and suddenly they will be wounded.
Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
8 Because of what they say [MTY], he will get rid of them, and then everyone who sees [what has happened to] them will shake their heads [to ridicule them].
Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
9 And then everyone will be afraid [to sin because of what might happen to them, also]; they will tell others what God has done, and they themselves will think much about it.
Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
10 Righteous people should rejoice because of what Yahweh [has done]; they should go to him to (find protection/be safe); and all those who are godly will praise him.
Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!