< Psalms 63 >

1 God, you are the God whom I [worship]. I greatly desire to be with you like [SIL] a person in a dry hot desert greatly desires [some cool water].
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2 So, I want to see you in your temple; I want to see that you are great and glorious.
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
3 Your constantly loving [me] is (worth more/more precious) than [my] life, so I [MTY] will [always] praise you.
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4 I will praise you all the time that I live; I will lift up my hands to you while I pray.
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5 [Knowing you satisfies me more than] [IDM, MET] my eating a very big feast, [so] I will praise you while I sing [MTY] joyful songs.
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6 While I lie on my bed, I think about you. I think/meditate about you all during the night,
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7 because you have always helped me, and I sing joyfully knowing that I am protected by you [as a little bird is protected] under [its mother’s] wings [MET].
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8 I cling to you; and with your hand/power you protect me.
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
9 But those who are trying to kill me will [die and] descend into the place of the dead;
Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
10 they will be killed in battles [MTY] and their [corpses] will be eaten by jackals/wild dogs.
Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
11 But I, the king [of Israel], will rejoice in what God has done; and all those who revere and trust God will praise him, but he will not allow liars to say anything.
Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.

< Psalms 63 >