< Psalms 55 >

1 God, listen to my prayer, and do not turn away from me while I am pleading with you.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Listen to me, and answer me, because I am overwhelmed by [all] my troubles.
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 My enemies cause me to be terrified; wicked people oppress me. They cause me to have great troubles; they are angry with me, and they hate me.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 I am terrified, and I am very much afraid that I will die.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 I am very fearful and I tremble/shake, and I am completely terrified.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 I said, “I wish that I had wings like a dove! If I had wings, I would fly away and find a place to rest.
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 I would fly far away and live in the desert.
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 I would quickly find a shelter from [my enemies] [who are like] [MET] a strong wind and rainstorm.”
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Lord, confuse my enemies, and cause their plans to fail, because I see them acting violently and causing strife in the city [of Jerusalem].
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 During [each] day and night they march around on top of its walls, committing crimes and causing trouble.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 They destroy [things] everywhere. They oppress and defraud [people] in the (marketplaces/public squares).
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 If it were an enemy who was making fun of me, I could endure it. If it were someone who hates me, who despises me, I could hide from him.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 But it is someone who is just like me, my companion, someone who was my friend [who is doing this to me].
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 We previously had many good talks together; we walked around together in God’s temple.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 I desire/hope that my enemies will die suddenly; while they are still young, cause them to go down to the place where the dead people are. They they think evil things. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 But I [will] ask Yahweh, [my] God, to help me, and he will save me.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 [Each] morning and [each] noontime and [each] evening I tell him what I am concerned about, and I moan, and he hears my voice.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 I have [very] many enemies, but he will rescue me and bring me back safely from the battles that I fight.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 God is the one who has ruled everything forever, and he will listen to me. He will cause my enemies to be [defeated and] disgraced, because they do not change their evil behavior and they do not revere God.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 My companion, [whom I mentioned previously], betrayed his friends and broke the agreement that he made with them.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 What he said was [easy to listen to, like] butter [is easy to swallow] [MET], but in his inner being he hated people; his words were [soothing] like [olive] oil, [but they hurt people like] sharp swords do [MET].
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Put your troubles in Yahweh’s hands, and he will take care of you; he will never allow righteous [people] to experience disasters.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 God, you will cause murderers [MTY] and liars to die before they have lived half as long as they expect to live; but [as for me], I will trust in you.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Psalms 55 >