< Psalms 50 >
1 God, the all-powerful one, speaks; he summons all people, from the east to the west.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 His glory shines from Zion [Hill in Jerusalem], an extremely beautiful city.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Our God comes to us, and he is not silent. A great fire is in front of him, and a storm is around him.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 He comes to judge his people. He shouts to the [angels in] heaven and to [the people on] the earth.
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 He says, “Summon those who faithfully [worship] me, those who made an agreement with me by offering sacrifices to me.”
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 The [angels in] heaven declare, “God is righteous, and he is the supreme judge.”
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 God says, “My people, listen! You Israeli people, listen, as I, your God, say what you have done that is wrong.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 I am not rebuking you for making sacrifices to me, for the offerings that you completely burn [on the altar].
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 But I do not really need [you to sacrifice] the bulls from your barns and the goats from your pens,
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 because all the animals in the forest belong to me, [and all] the cattle on 1,000 hills also belong to me.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 I [own and] know all the birds and all [the creatures] that move around in the fields.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 [So], if I were hungry, I would not tell you [to bring me some food], because everything in the world belongs to me!
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 I do not eat the flesh of the bulls [that you sacrifice], and I do not drink the blood of the goats [that you offer to me].
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 The sacrifice [that I really want is that] you thank me and do all that you have promised to do.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 And pray to me when you have troubles. [If you do that], I will rescue you, and [then] you will praise me.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 But I say this to the wicked people: (Why do you/It does not benefit you at all to) [RHQ] recite my commandments or talk about the agreement that I made with you,
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 because you have refused to allow me to discipline you, and you have rejected what I told you to do.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Every time that you see a thief, you become his friend, and you spend [much] time with those who commit adultery.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 You are [always] talking [MTY] about doing wicked things, and you are [always] to deceive people.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 You are always accusing members of your own family [of doing wrong], and slandering them.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 You did [all] those things, and I did not say anything to you, [so] you thought that I was [a sinner] just like you. But now I rebuke you and accuse you, right in front of you.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 So, all you who have ignored me, pay attention to this, because if you do not, I will tear you to pieces, and there will be no one to rescue you.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 The sacrifice that [truly] honors me is to thank me [for what I have done]; and I will save those who always do the things that I want them to.”
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”