< Psalms 48 >
1 Yahweh is great, and he deserves to be greatly praised in the city where he [lives], [which is built on Zion], his sacred hill.
Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
2 That city, on a high [hill], is beautiful; it is the city where the true [God], the great king, [lives], and it causes people all over the world to rejoice [when they see it].
Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
3 God is in the strong towers there, and he shows that he protects the people in that city.
Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
4 Many kings gathered [with their armies] to attack [that city],
Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
5 but when they saw it, they were amazed; they became terrified, and ran away.
sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
6 Because they were very afraid, they trembled like a woman who is about to give birth to a child;
Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
7 they shook [like] ships sailing from Tarshish are shaken by a strong wind.
Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
8 We had heard [that this city is glorious], and now we have seen that it is. It is the city in which Yahweh, the almighty one, [lives]. It is the city which God will preserve/protect forever.
Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
9 God, [here] in your temple we think about how you faithfully love us.
Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
10 You [MTY] are famous and (are praised/people praise you) all over the earth, because you rule powerfully [MTY] and justly.
Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
11 The people who live near Zion Hill should be happy! The people in [all] the cities [MTY] in Judah should rejoice because you judge people fairly.
Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
12 [You Israeli people should] walk around Zion [Hill] and count the towers there;
Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
13 notice the walls there and examine the forts in order that you can tell about them to your children.
ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
14 [Say to them], “This is [the city that belongs to] our God, [the one who lives] forever; he will guide us all of our lives.”
Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.