< Psalms 42 >

1 Deer pant, desiring to drink water from a stream [when there is a drought] (OR, [when they are being pursued by hunters].) In the same way [SIM], God, I need you very much.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
2 I desire to have fellowship with [MET] you, the all-powerful God. [I wonder], “When will I be able to go [back to the temple in Israel] and worship in your presence again?”
Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
3 Every day and every night I cry; [it is as though] the only thing I have to drink is my tears; and while I do that, my enemies are continually asking me, “Why does your god not [help you]?”
Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
4 I am very distressed [IDM] as I remember when I went with the crowd of people to the temple [in Jerusalem], leading them as we walked along; we were all shouting joyfully and singing to thank God [for what he had done]; we were a large group who were celebrating.
Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
5 So [I say to] myself, “(Why am I sad and discouraged?/I should not be sad and discouraged!) [RHQ] I confidently expect God [to help me], and again I will praise him, my God, the one who saves me.”
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
6 [But now, Yahweh], I am very discouraged [IDM], so I think about you, even from where the Jordan [River] gushes out from the bottom of Hermon [Mountain] and from Mizar Mountain.
Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
7 But here, the great sorrow that I feel is like water that you send down [MET]; [it is like] a waterfall that tumbles down and floods over me.
Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
8 Yahweh shows me each day that he faithfully loves me, and each night I sing to him and pray to him, the God who causes me to live.
Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
9 I say to God, [who is like] an [overhanging] rock [under which I can hide] [MET], “It seems that you have forgotten me. I (mourn/cry) constantly because my enemies act cruelly toward me” [RHQ].
Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
10 They make fun of me constantly; they continually ask, “Why does your god not help you?” [RHQ] And when they insult me [like that], [it is like] wounds that I feel even in my bones.
Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
11 But [I think, ] “(Why am I sad and discouraged?/I should not be sad and discouraged!) [RHQ] I will confidently expect God [to help me], and I will praise him again, my God, the one who saves me.”
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.

< Psalms 42 >