< Psalms 41 >

1 Yahweh is pleased with those people who help to provide for the poor; he will rescue those people when they have troubles.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
2 Yahweh protects them and allows them to live [for a long time]. He enables them to be happy in the land [of Israel], and rescues them from their enemies.
Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
3 When they are sick, Yahweh strengthens them, and he heals them.
Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
4 [When I was sick], I said, “Yahweh, be merciful to me and heal me; [I know that I am sick because] I have sinned against you.”
Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
5 My enemies say cruel things about me; they say, “How soon will he die, and then everyone will forget about him [MTY]? (OR, he will not have [any descendants to continue] his name).”
Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
6 When my enemies come to me, they falsely say that they [are concerned about me]. They listen to bad news about (me/my health). Then they go away and tell everywhere what is happening to me.
Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
7 All those who hate me whisper to others about me, and they hope/desire that very bad things will happen to me.
Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
8 They say, “He will soon die because of his being sick; he will never get up from his bed [before he dies].”
“Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
9 Even my best friend, whom I trusted very much, who [often] ate with me, has (betrayed me/put me into my enemies’ hands) [IDM].
Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
10 But Yahweh, be merciful to me, and enable me to become healthy [again]. When you do that, I will be able to (pay back my enemies/get revenge on my enemies/cause my enemies to suffer like they caused me to suffer).
Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
11 [If you enable me to] do that, with the result that my enemies do not defeat me, I will know that you are pleased with me.
Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12 [I will know that] it is because I have done what is right that you have helped me, and [I will know that] you will let me be with you forever.
Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13 Praise Yahweh, the God whom we Israelis [worship]; Praise him forever! Amen! I desire that it will be so!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.

< Psalms 41 >