< Psalms 40 >
1 I waited patiently for Yahweh [to help me], and he listened to me [DOU] when I called out to him.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
2 [When I had many troubles, it was as though] I was in a deep pit. But he lifted me up out of the mud and slime of that pit; he set my feet on a [solid] rock, and enabled me to walk (safely/without falling).
Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
3 He has given me a new song to sing, a song to praise him who is our God. Many people will find out [what he has done for me], and they will revere and trust him.
Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
4 Yahweh is pleased with those who trust him, those who do not trust in idols or join with those who worship those false gods.
Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
5 O Yahweh, my God, you have done many wonderful things! No one can list all the wonderful things that you have planned for us. If I tried to tell [others] about all those wonderful things, I would not be able to, because there would be too many for me to mention.
Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
6 Various kinds of sacrifices and other offerings are not the [only] things that delight you. You have enabled me to understand that very well [IDM]. [Animals] burned [on the altar] and [other] offerings are not all that you require [for sins to be forgiven].
Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
7 So I said [to you], “Yahweh, here I am, [to do] the things that have been written in the scroll [that contains your laws], things that you want me [to do].”
Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
8 O my God, I delight to do what you desire; I [keep] your laws within my inner being.
Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
9 Whenever all [your people] are gathered, I have told them about how you save us. Yahweh, you know that I have not been afraid to tell that to them.
Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
10 And I have not kept to myself the news that you always act justly/fairly; when many of your people have gathered together [to worship you in the temple], I have told them that you are faithful to us and save us. I have (not concealed/openly told people) that you faithfully love us and act loyally toward us.
Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
11 Yahweh, do not stop being merciful to me. Because you faithfully love [me] [PRS] and are loyal [to me], always protect me.
Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
12 I have many troubles; [so many that] I cannot count them. My sins are like a flood that has covered me [PRS, MET]; [they are so many that] I cannot find my way. The sins that I have committed are more than the hairs on my head. I am very discouraged.
Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
13 O Yahweh, please save me! Come quickly to help me!
Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
14 Humble those who are happy about my troubles, and cause them to be disgraced and ashamed. Chase away those who are trying to get rid of me.
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
15 I hope/desire that those who make fun of me will be dismayed when you defeat them.
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
16 But I hope that all those who go to [worship] you will be very joyful [DOU]. I want those who love you because you saved them to shout repeatedly, “Yahweh is great!”
Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
17 As for me, I am poor and needy [DOU]; but [I know that] Yahweh has not forgotten me. O my God, you are the one who saves and helps me, so please come quickly [and help me!]
Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.